Yadda Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass ya yi wa Tinubu addu’ar nasara
Published: 1st, February 2025 GMT
Shugabannin Ɗariƙar Tijjaniyya bisa jagorancin Khalifa Sheikh Muhammad Mahi Inyass, sun ziyarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadarsa.
A yayin ziyarar, Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass kuma ɗansa, Khalifa Sheikh Muhammad Mahi, da tawagarsa sun halarci Sallar Juma’a tare da Shugaba Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa.
Malaman sun kuma gudanar da addu’o’in neman taimakon Allah da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci-gaba da kuma albarka ga Najeriya.
Khalifa Muhammad Mahi Inyass, ɗa ga Jagoran Tijjaniyya Sheikh Ibrahim Inyass, ya jinjina wa Gwamnatin Tinubu, inda ya yi wa shugaban ƙasa addu’ar samun nasara da ƙarin basira da nasara a shugabanci domin kawo gagarumar ci-gaba a Najeriya.
Masu yi wa ƙasa hidima za su karɓi N77,000 daga Fabrairu – Shugaban NYSC ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a ZamfaraKhalifa Mahi Inyass ya shaida wa manema labarai cewa tawagar ta taso ne musamman daga ƙasar Senegal, mahaifar Sheikh Ibrahim Inyass, domin halartar Maulidin Tijjaniyya na Sheikh Inyass na wannan shekara.
Ya ba wa Shugaba Tinubu tabbacin goyon baya da addu’o’i musamman daga mabiya ɗarikar Tijjaniyya sam da miliyan 400 da ke Najeriya da sauran wurare.
’Yan tawagar sun haɗa da Sheikh Ibrahim, babban ɗan Sheikh Dahiru Usman Bauchi, da dai sauran shugabannin Ɗariƙar Tijjaniyya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Darikar Tijjaniyya Inyass Mahi Ibrahim Inyass Tijjaniyya Sheikh Ibrahim Inyass
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
Shugaban Palasdinu da kuma kungiyar kwatar yencin falasdinawa PLO Mahmud Abbas ya nada magajinsa da kuma wasu mataimaka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran, ta bayyana cewa Abbas dan shekara 89 ya nada mataimakinsa ne bayan taron majalisar gudanarwa ta gwamnatinsa a makon da ya gabata.
Labarin ya kara da cewa kasashen yamma da yankin sun dade suna takurawa Abbas kan ya nada mataimaki da kuma wasu mataimaka sabuda rawar da gwamnatinsa zata taka bayan yakin gaza.
A yau ne majalisar zartarwa ta amince da nada Hussein Al Sheikh a matsayin mataimakin shugaban majalisar da kuma mataimakin shugaban kasa a lokaci guda.
Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Falasdinawan WAFA, ya bayyana cewa gwamnatin Abbas ce da hakkin sa hannu a kan yarjeniyoyi da suka shafi Falasdinu, a madadin dukkan kungiyoyin Falasdinawa, banda wadanda su ka dauke da makamai suna yakar HKI, wato Hamas da kuma Jihadul Islami a Gaza.
Mr Al Sheikh, dan shekara 64 a duniya na hannun daman Abbas ne a kungiyarsa ta fatah.