Aminiya:
2025-09-18@06:57:18 GMT

Gwamna Buni ya zama Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Tafkin Chadi

Published: 31st, January 2025 GMT

Gwamnonin tafkin Chadi da suka haɗa da Nijeriya da Nijar da Kamaru da Chadi, sun zaɓi gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a matsayin sabon shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin.

Sanarwar na cewar, an zaɓi Gwamna Buni ne a ranar Juma’a a ƙarshen taron ƙungiyar gwamnonin tafkin Chadi karo na 5 da aka gudanar a Maiduguri.

’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a Zamfara Direba cikin barasa ya murƙushe sojoji sun mutu a Legas

Tun farko shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne wanda mataimakin shugabansa Kashim Shettima ya wakilta ya bayyana buɗe taron da gwamnatin Jihar Yobe ta shirya.

Gwamna Buni a jawabinsa na karramawa ya yaba wa shugaba Tinubu bisa yadda ya samar da jagoranci ga ƙasa da yankin a cikin mawuyacin hali.

Ya gode wa takwarorinsa Gwamnonin yankin tafkin Chadi, da wakilai da sauran masu ruwa da tsaki saboda halartar taron da kuma bayar da gudunmawarsu wajen samun nasarar taron.

“Ina miƙa godiya ta ga mai girma shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa jagorancinsa da jajircewarsa wajen samar da zaman lafiya da tsaro da ci gaban yankin tafkin Chadi.”

“Ina da yaƙinin cewa, mun sanya zamanmu a nan a cikin ‘yan kwanakin nan ya zama abin tunawa da albarka tare da yin adalci a kan taken taron “Sake gina tafkin Chadi: Ƙarfafa Ci gaban yankin, sadaukar da kai ga zaman lafiya, haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen yankin, tsaro da ci gaba mai ɗorewa ga al’ummar yankin.” in ji shi.

Gwamnan ya bayyana fatansa yana mai cewa “a matsayina na mai masaukin baki ina fatan za mu aiwatar da dukkan darussa da ƙudurorin wannan taro  don ci gaban wannan yanki.

“Saboda haka, muna sa ran samun ƙarin haɗin gwiwa, tallafi da rabon albarkatun da ake buƙata don aiwatar da burinmu na gina kyakkyawan yanki mai wadata ga jama’armu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya da Nijar da Kamaru da Chadi

এছাড়াও পড়ুন:

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Ya ce kuma kayan da ake fitarwa zuwa waje waɗanda ba man fetur yanzu su kusa yin kai da kai da fetur.

Ya ƙara da cewa ajiyar kuɗaɗen ƙasar a waje ya haura kusan dala biliyan 42, daga biliyan 32 lokacin da Tinubu ya hau mulki.

Har ila yau, ya ce an biya bashin da ya haura biliyan bakwai, ciki har da miliyan 800 da ake bin jiragen saman Nijeriya.

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yanzu jihohi na iya biyan albashi da fansho a kan lokaci, sannan suna da rarar kuɗi don ayyukan raya ƙasa, abin da ba a saba gani ba a baya.

“Bayan shekara biyu da watanni biyar kacal a ofis, Shugaba Tinubu ya cimma abubuwa da dama. Ko da Atiku da magoya bayansa ba su yadda ba, ’yan Nijeriya suna ganin sauyin,” in ji Onanuga.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma zargi Atiku da jam’iyyar PDP da yaɗa maganganun da za su kawo tashin hankali.

Ya bayyana cewa yawancin matsalolin da ake fuskanta sun samo asali ne daga rashin kyakkyawan shugabanci tun a lokacin PDP, lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara