Gwamna Buni ya zama Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Tafkin Chadi
Published: 31st, January 2025 GMT
Gwamnonin tafkin Chadi da suka haɗa da Nijeriya da Nijar da Kamaru da Chadi, sun zaɓi gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a matsayin sabon shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin.
Sanarwar na cewar, an zaɓi Gwamna Buni ne a ranar Juma’a a ƙarshen taron ƙungiyar gwamnonin tafkin Chadi karo na 5 da aka gudanar a Maiduguri.
Tun farko shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne wanda mataimakin shugabansa Kashim Shettima ya wakilta ya bayyana buɗe taron da gwamnatin Jihar Yobe ta shirya.
Gwamna Buni a jawabinsa na karramawa ya yaba wa shugaba Tinubu bisa yadda ya samar da jagoranci ga ƙasa da yankin a cikin mawuyacin hali.
Ya gode wa takwarorinsa Gwamnonin yankin tafkin Chadi, da wakilai da sauran masu ruwa da tsaki saboda halartar taron da kuma bayar da gudunmawarsu wajen samun nasarar taron.
“Ina miƙa godiya ta ga mai girma shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa jagorancinsa da jajircewarsa wajen samar da zaman lafiya da tsaro da ci gaban yankin tafkin Chadi.”
“Ina da yaƙinin cewa, mun sanya zamanmu a nan a cikin ‘yan kwanakin nan ya zama abin tunawa da albarka tare da yin adalci a kan taken taron “Sake gina tafkin Chadi: Ƙarfafa Ci gaban yankin, sadaukar da kai ga zaman lafiya, haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen yankin, tsaro da ci gaba mai ɗorewa ga al’ummar yankin.” in ji shi.
Gwamnan ya bayyana fatansa yana mai cewa “a matsayina na mai masaukin baki ina fatan za mu aiwatar da dukkan darussa da ƙudurorin wannan taro don ci gaban wannan yanki.
“Saboda haka, muna sa ran samun ƙarin haɗin gwiwa, tallafi da rabon albarkatun da ake buƙata don aiwatar da burinmu na gina kyakkyawan yanki mai wadata ga jama’armu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya da Nijar da Kamaru da Chadi
এছাড়াও পড়ুন:
Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
Hukumar zaben kasar Tanzaniya ta bayyana shugabar kasa mai ci Samia Suluhu Hassan a matsayin wadda ta lashe zaben shugaban kasar.
Shugaban hukumar zaben ya ce Shugaba Samia ta yi nasara a zaben da kashi 98% na jimillar kuri’un da aka kada.
Bayanai sun ce manyan ‘yan takarar adawa ba su shiga ba, wasu kuma an tsare su ko kuma an hana su tsayawa takara, wanda hakan ya haifar da tashin hankali.
Jam’iyyar adawa ta kasar ta ce daruruwan mutane ne suka mutu sanadiyyar zanga-zangar da aka kwashe kwanaki ana yi tun bayan zaben na ranar Laraba.
Wani mai magana da yawun jam’iyyar adawa ta Chadema ya shaida wa AFP cewa kimanin mutane 700 ne suka mutu, a alkalumman da aka tattara daga asibitoci.
Gwamnatin Shugaba Samia ta musanta duk wani “yin amfani da karfi fiye da kima,” yayin da Ministan Harkokin Waje Mahmoud Thabit Kombo ya shaida wa Al Jazeera cewa babu “bayani” kan adadin wadanda suka mutu.
Hukumomin sun katse hanyar intanet, sun sanya dokar hana fita, kuma sun takaita ‘yan jarida, wanda hakan ya takaita samun bayanai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci