Aminiya:
2025-07-31@18:03:29 GMT

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 10 ta kama 12 bayan musayar fursunoni 110

Published: 31st, January 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta sanar da sunayen mutum uku da za ta mika wa kasar Isra’ila a Gaza a ranar Asabar a ci gaba da musayar fursunonin yaki tsakaninsu.

Bayan sako ’yan Isra’ila uku da ’yan kasar Thailand biyar a ranar Alhamis, Rundunar Qassam , sashen sojin Hamas ta sanar ranar Juma’a cewa wadanda kungiyar za ta sako su ne Ofer Kalderon da Keith Siegel da kuma Yarden Bibas.

Hakan na zuwa ne bayan a cikin dare jiragen yakin Isra’ila sun kashe Palasdinawa 10 a sansanin ’yan gudun hijira na Jenin da ke garin Tammun da ke yankin Yammacin Kogin Jordan.

Kazailka ’yan sandan Isra’ila sun kama Palasdinawa 12 a yankin Gabashin Birnin Kudus a yayin da suke murnar sako ’yan uwansu 110 da Isra’ila ta yi daga gidajen yarinta a wani bangare na yarjejeniyar zaman lafiya a Zirin Gazan.

An ɗaure zawarawa a gidan yari kan aikata zina Tubabbun ’yan Boko Haram 5,000 sun koma cikin jama’a

Jami’an tsaro na Isra’ila na ci gaba da kai hare hare da tsare Palasdinawa ne duk yarjejeniyar zaman lafiyar da ake aiwatarwa a Zirin Gazan.

Kawo yanzu Palasdinawa 47,460 ne aka kashe, tare da jikkata wasu  111,580 tun daga ranar 7 ga Oktoban 2023 da aka fara wannan yaki.

An kashe wasu kimanin 1,139 a Isra’ila a lokacin da kungiyar Palasdinawa ta Hamas ta kai hai a ranar, inda ta yi garkuwa da wasu kimanin 200, ciki har da baki ’yan kasashen waje.

‘Yan sandan Isra’ila sun kama wasa Palasdinawa 12 da ke murnar sako ’yan uwansu 110 daga gidajen yarin Isra’ila a wani bangare na yarjejeniyar zaman lafiya a Zirin Gazan.

Jami’an tsaron Isra’ilar sun tsare mutanen ne a yankin Gabashin Birnin Kudus saboda suka murnar sako Palasdinawa da Isra’ila ta tsare a gidajen yarinta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Palasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Makama Hardawa, ya rasu.

Marigayin ya rasu ne ranar Talata a Abuja, bayan ya yi fama da gajeruwar jinya.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ne ya tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza