ECOWAS : Kofarmu A Bude Take Ga Al’ummun Kasashen Burkina, Mali Da Nijar
Published: 30th, January 2025 GMT
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ce kofar kasashe mambobinta a bude take domin shige da ficen al’ummun kasashen kawancen Sahel da suka balle daga cikinta wato Burkina Faso, Mali da Nijar.
A wata sanarwar da ta fitar ranar Laraba a shafinta na X, ECOWAS ta ce duk da cewar daga ranar Laraba 29 ga watan Janairun shekarar 2025 ne ficewar kasashen daga ECOWAS ta tabbata, tana kira ga kasashe mambobinta su saurara wa al’ummmun kasashen uku.
Sanarwar ta ce saboda hadin kai na yankin da amfanin jama’a da kuma shawara da muhukuntan ECOWAS suka yanke ta barin kofar kungiyar a bude, ECOWAS za ta ci gaba da amincewa da fasfo din ‘ya’yan kasashen da ke dauke da tambarin ECOWAS.
Ta kara da cewa ta nemi dukkan ƙasashen ECOWAS su ci gaba da bin tsarin sassaucin kasuwanci bisa shige da fice na kayayyaki da ma’aikata daga kasashen AES zuwa kasashen ECOWAS.
Kazalika ECOWAS ta nemi kasashen su ba da hadin kai ga jami’an ECOWAS daga kasashen a ciki aikin su ga ECOWAS, har zuwa lokacin da shugabannin kasashen ECOWAS za su yanke shawara game da irin huldar da za su yi da kasashen uku.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta Zuwa Waje
Mai magana da yawun hukumar da take kula da filin saukar jiragen sama ta Ben Gorion ta sanar a yau Asabar cewa an rufe filin saukar jiragen saman har zuwa wani lokaci a nan gaba, bayan da aka dauke dukkanin jiragen sama zuwa kasashen Cyprus, Greece da kuma Amurka.
Mai Magana da yawun hukumar filin saukar jiragen saman na Ben Gorion Lisa Daiper ta bayyana ce; Babu wani lokaci takamaimai da aka tsayar domin sake bude filin saukar jiragen saman na Ben Gorion.”
A gefe daya jaridar “Maariv’ ta bayyana cewa; An dauke dukkanin jiragen sama zuwa filayen jiragen saman a kasashen turai.
Haka nan kuma ta kara da cewa; An dauki 14 daga cikin jiragen saman na HKI zuwa filin saukar jiragen saman a Laranka da Papus dake tsibirin Cyprus da su ne filayen jiragen sama na nahiyar turai mafi kusa da HKI.
Su kuwa jiragen da shugabannin ‘yan sahayoniya suke shiga an kai su ne zuwa filin jirgin sana na birnin Athenia na kasar Girka, wasu kuwa zuwa kasashen Bulgari da Faransa.
Dauke jiragen na ‘yan sahayoniya dai ya zo ne saboda tsoron kar makamai masu linzami na Iran su isa gare su.