HausaTv:
2025-11-03@04:00:52 GMT

ECOWAS : Kofarmu A Bude Take Ga Al’ummun Kasashen Burkina, Mali Da Nijar

Published: 30th, January 2025 GMT

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ce kofar kasashe mambobinta a bude take domin shige da ficen al’ummun kasashen kawancen Sahel da suka balle daga cikinta wato Burkina Faso, Mali da Nijar.

A wata sanarwar da ta fitar ranar Laraba a shafinta na X, ECOWAS ta ce duk da cewar daga ranar Laraba 29 ga watan Janairun shekarar 2025 ne ficewar kasashen daga ECOWAS ta tabbata, tana kira ga kasashe mambobinta su saurara wa al’ummmun kasashen uku.

Sanarwar ta ce saboda hadin kai na yankin da amfanin jama’a da kuma shawara da muhukuntan ECOWAS suka yanke ta barin kofar kungiyar a bude, ECOWAS za ta ci gaba da amincewa da fasfo din ‘ya’yan kasashen da ke dauke da tambarin ECOWAS.

Ta kara da cewa ta nemi dukkan ƙasashen ECOWAS su ci gaba da bin tsarin sassaucin kasuwanci bisa shige da fice na kayayyaki da ma’aikata daga kasashen AES zuwa kasashen ECOWAS.

Kazalika ECOWAS ta nemi kasashen su ba da hadin kai ga jami’an ECOWAS daga kasashen a ciki aikin su ga ECOWAS, har zuwa lokacin da shugabannin kasashen ECOWAS za su yanke shawara game da irin huldar da za su yi da kasashen uku.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

 

Shugaba Xi ya kara da cewa, a halin da ake ciki yanzu, duniya na fuskantar sauye-sauye irin wadanda ba a taba gani ba kuma cikin sauri. Don haka, kamata ya yi kasashen biyu masu dadaddun wayewar kai su zurfafa koyi da juna, da shigar da sabon kuzari cikin gina cikakken salon hadin kai, bisa manyan tsare-tsare tsakaninsu, kana su tattaro karfin wayewar kai don gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama.

 

A wani ci gaban kuma, wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping wato ministan raya al’adu da yawon bude ido na kasar Sun Yeli, ya halarci bikin bude babban gidan adana kayan tarihin na GEM bisa gayyatar gwamnatin Masar. Kafin bikin, shugaba al-Sisi ya gana tare da gudanar da gajeriyar tattaunawa da Sun Yeli. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik November 2, 2025 Daga Birnin Sin Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik November 2, 2025 Daga Birnin Sin An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare