ECOWAS : Kofarmu A Bude Take Ga Al’ummun Kasashen Burkina, Mali Da Nijar
Published: 30th, January 2025 GMT
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ce kofar kasashe mambobinta a bude take domin shige da ficen al’ummun kasashen kawancen Sahel da suka balle daga cikinta wato Burkina Faso, Mali da Nijar.
A wata sanarwar da ta fitar ranar Laraba a shafinta na X, ECOWAS ta ce duk da cewar daga ranar Laraba 29 ga watan Janairun shekarar 2025 ne ficewar kasashen daga ECOWAS ta tabbata, tana kira ga kasashe mambobinta su saurara wa al’ummmun kasashen uku.
Sanarwar ta ce saboda hadin kai na yankin da amfanin jama’a da kuma shawara da muhukuntan ECOWAS suka yanke ta barin kofar kungiyar a bude, ECOWAS za ta ci gaba da amincewa da fasfo din ‘ya’yan kasashen da ke dauke da tambarin ECOWAS.
Ta kara da cewa ta nemi dukkan ƙasashen ECOWAS su ci gaba da bin tsarin sassaucin kasuwanci bisa shige da fice na kayayyaki da ma’aikata daga kasashen AES zuwa kasashen ECOWAS.
Kazalika ECOWAS ta nemi kasashen su ba da hadin kai ga jami’an ECOWAS daga kasashen a ciki aikin su ga ECOWAS, har zuwa lokacin da shugabannin kasashen ECOWAS za su yanke shawara game da irin huldar da za su yi da kasashen uku.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Yau Laraba 30 ga wata, an kira taro a ofishin siyasa na kwamitin koli na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS), inda aka yanke shawarar gudanar da cikakken zama na 4 na kwamitin koli na 20 na JKS a watan Oktoba na shekarar da muke ciki, domin nazari kan shawarar tsara shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15.
Taron ya nuna cewa, lokacin gudanar da “Shirin shekaru biyar-biyar din na 15”, lokaci ne mai muhimmanci a fannin tabbatar da ingantaccen tushe, da kokarin raya zamanantar da kasar Sin bisa tsarin gurguzu. A yanzu haka yanayin ci gaban kasar Sin yana fuskantar manyan sauye-sauye masu sarkakiya, akwai kuma damarmaki bisa manyan tsare-tsare da ma kalubale tare.
A waje guda kuma, tattalin arzikin kasar yana da tushe mai karko, da tarin fifiko, da karfin juriya, da kuma makoma mai kyau a nan gaba. Har ila yau, fifikon da kasar Sin ke da shi a fannonin tsarin gurguzu mai halin musamman irin na kasar, da kasuwa mai girma sosai, da cikakken tsarin masana’antu, da kuma albarkatun kwararru, ya fi bayyana sosai.
Taron ya kuma nuna cewa, kamata ya yi a kara azamar cimma nasara, da gudanar da ayyuka yadda ya kamata, don samun rinjaye bisa manyan tsare-tsare a yayin da Sin ke shiga takara a duniya, da ma samun babban ci gaba a ayyukan da suka shafi zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp