Rundunar Ƴansandan Kano Ta Kori Wani Jami’in Saboda Karɓar Na Goro
Published: 30th, January 2025 GMT
Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta kori wani jami’in sa-kai, Ado Abba, bisa zargin gudanar da bincike ba bisa ƙa’ida ba da kuma karɓar kudin haram daga jama’a.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana hakan a wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ake ganin korarren jami’in tsaye a gefensa domin tabbatar da an san shi.
Ya kara da cewa za a kwace kayayyakin sa-kai daga hannunsa, sannan ya buƙaci jama’a su riƙa kai rahoton duk wani laifi da jami’an ‘yansanda suka aikata. SP Kiyawa ya yaba wa sauran jami’an sa-kai bisa ƙoƙarinsu wajen tabbatar da tsaro a Kano, tare da yin kira da su ci gaba da aiki da gaskiya da ƙwarewa.
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
Ya ce, masu garkuwa da mutanen sun afka gidansa ne a daren Lahadi a lokacin da mazauna gidan ke shirin kwanciya barci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp