Shugaban kasar Amurka ya rattaba hannu kan dokar ba da damar tsare bakin haure kusan 30,000 a sansanin Amurka da ke tsibirin Guantanamo

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana son gidan kurkukun sojoji da ke Guantanamo Bay, wanda aka kebance domin tsare fursunonin da ake zargi da ta’addanci, ya kasance a shirye domin karban bakin haure kusan 30,000 da suka shiga cikin Amurka ba bisa ka’ida ba.

Trump yana cewa: “A yau zai rattaba hannu kan wani umarni na zartarwa wanda ke umurtar ma’aikatar tsaro da tsaron cikin gida da su shirya wata cibiya da za ta karbi bakin haure 30,000 a tsibirin Guantanamo Bay,” Trump ya kara da cewa: Guantanamo zai karbi “masu aikata laifuka” a cikin wani yanayi na yau da kullun ba na sojojin yaki ba.

Shugaban na Amurka ya kuma rattaba hannu kan dokarsa ta farko tun bayan hawansa mulki a ranar 20 ga watan Janairu, wani mataki na nuna adawa da shige da fice wanda ke ba da damar tsare mutane kai tsaye a cikin wani yanayi da ba na soji ba idan aka tuhume su ko kuma aka yi musu shari’a a kan aikata wasu laifuffuka ko keta hurumin wasu dokoki.

An bude gidan yarin na Guantanamo ne a shekara ta 2002, a cikin wani sansanin sojin Amurka da ke Cuba, a matsayin wani bangare na yaki da ta’addanci da tsohon shugaban Amurka George W. Bush ya ayyana bayan kai harin ranar 11 ga watan Satumban shekara ta 2001.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona da ke Sipaniya na ƙoƙarin ɗauko Victor Osimhen a matsayin wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski wanda ke fama da matsalar raunuka

Ɗan jaridar ƙasar Sifaniya, Gabriel Sans na Mundo Deportivo ya bayyana cewar, Barcelona na neman wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski a matsayin mai jefa ƙwallo a raga, hakan ne ya sa ƙungiyyar ta amince da ɗaukar Osimhen.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

A ƙarshen kakar bana ne ake tunanin up Lewandowski zai bar Barca, wanda zai tilasta wa ƙungiyyar neman wani zaƙaƙurin ɗan wasan gaba mai ciyo ƙwallo.

Victor Osimhen dai a bazarar nan ne ya koma Galatasaray bayan barin Napoli ta Italiya.

Osimhen dai ba ya ɓoye aniyarsa ta buga wasa a ɗaya daga cikin manyan gasannin Nahiyyar Turai biyar ba, ciki har da Firimiya ta Ingila da LaLiga ta Sifaniya, inda Barcelona ke cikin manyan ƙungiyoyin gasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure