Shugaban kasar Amurka ya rattaba hannu kan dokar ba da damar tsare bakin haure kusan 30,000 a sansanin Amurka da ke tsibirin Guantanamo

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana son gidan kurkukun sojoji da ke Guantanamo Bay, wanda aka kebance domin tsare fursunonin da ake zargi da ta’addanci, ya kasance a shirye domin karban bakin haure kusan 30,000 da suka shiga cikin Amurka ba bisa ka’ida ba.

Trump yana cewa: “A yau zai rattaba hannu kan wani umarni na zartarwa wanda ke umurtar ma’aikatar tsaro da tsaron cikin gida da su shirya wata cibiya da za ta karbi bakin haure 30,000 a tsibirin Guantanamo Bay,” Trump ya kara da cewa: Guantanamo zai karbi “masu aikata laifuka” a cikin wani yanayi na yau da kullun ba na sojojin yaki ba.

Shugaban na Amurka ya kuma rattaba hannu kan dokarsa ta farko tun bayan hawansa mulki a ranar 20 ga watan Janairu, wani mataki na nuna adawa da shige da fice wanda ke ba da damar tsare mutane kai tsaye a cikin wani yanayi da ba na soji ba idan aka tuhume su ko kuma aka yi musu shari’a a kan aikata wasu laifuffuka ko keta hurumin wasu dokoki.

An bude gidan yarin na Guantanamo ne a shekara ta 2002, a cikin wani sansanin sojin Amurka da ke Cuba, a matsayin wani bangare na yaki da ta’addanci da tsohon shugaban Amurka George W. Bush ya ayyana bayan kai harin ranar 11 ga watan Satumban shekara ta 2001.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta

Kasar Amurka ta sanar da dakatar da bai wa mutanen Nijar bisa ta shiga cikin kasarta har illa masha Allahu.

Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka ne ya tabbatar da cewa an dakatar da bayar da bisa din ga ‘yan kasar Nijar da suke son shiga cikin kasar, saboda abinda ya kira matsala da ake da ita da gwamnatin Nijar, ba tare da yin Karin bayani ba.

 Sai dai kuma sanarwar ta yi togiya akan jami’an diflomasiyya da sauran jami’an gwamanti,kamar yadda wani sako na diplomasiyya ya nuna a ranar 25 ga watan Yuli.

Wannan matakin na  Amurka ya biyo byan rashin jituwar da ake da shi a tsakanin gwamatin Amurka da gwamnatin Jamhuriyar Nijar. A watan Satumba da ya shude ne dai Amurka ta kammala dauke sojojinta daga kasar Nijar bayan da gwamnatin sojan kasar ta umarce su, su fice daga kasar.

Da akwai sojojin Amurka da sun kai 1000 a cikin jamhuriyar Nijar, da janye su yake a matsayin kwankwasar kan Amurka da rage tasirinta a yammacin Afirka.

Gabanin juyin mulkin da aka yi a kasar dai Amurka tana amfani da wannan cibiyar a abinda take kira fada da ta’addaci a yammacin Afirka. Sai dai kuma hakan bai hana ci gaba da yaduwar ayyukan ta’addanci a cikin kasashen na yammacin Afirka ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta