Shugaban kasar Amurka ya rattaba hannu kan dokar ba da damar tsare bakin haure kusan 30,000 a sansanin Amurka da ke tsibirin Guantanamo

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana son gidan kurkukun sojoji da ke Guantanamo Bay, wanda aka kebance domin tsare fursunonin da ake zargi da ta’addanci, ya kasance a shirye domin karban bakin haure kusan 30,000 da suka shiga cikin Amurka ba bisa ka’ida ba.

Trump yana cewa: “A yau zai rattaba hannu kan wani umarni na zartarwa wanda ke umurtar ma’aikatar tsaro da tsaron cikin gida da su shirya wata cibiya da za ta karbi bakin haure 30,000 a tsibirin Guantanamo Bay,” Trump ya kara da cewa: Guantanamo zai karbi “masu aikata laifuka” a cikin wani yanayi na yau da kullun ba na sojojin yaki ba.

Shugaban na Amurka ya kuma rattaba hannu kan dokarsa ta farko tun bayan hawansa mulki a ranar 20 ga watan Janairu, wani mataki na nuna adawa da shige da fice wanda ke ba da damar tsare mutane kai tsaye a cikin wani yanayi da ba na soji ba idan aka tuhume su ko kuma aka yi musu shari’a a kan aikata wasu laifuffuka ko keta hurumin wasu dokoki.

An bude gidan yarin na Guantanamo ne a shekara ta 2002, a cikin wani sansanin sojin Amurka da ke Cuba, a matsayin wani bangare na yaki da ta’addanci da tsohon shugaban Amurka George W. Bush ya ayyana bayan kai harin ranar 11 ga watan Satumban shekara ta 2001.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Daga ranar 14 zuwa 15 ga wata, an gudanar da sabon zagayen shawarwari kan harkokin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka a birnin Madrid, babban birnin kasar Spaniya, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra’ayoyi a kan harkokin cinikayya da ke janyo hankalinsu, tare da cimma daidaito ta fannin daidaita batutuwan da suka shafi Tiktok, da rage shingayen zuba jari, da sa kaimin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu.

Taron shawarwarin ya kasance zagaye na hudu da sassan biyu suka gudanar cikin watanni biyar da suka wuce. Kwatankwacin shawarwarin da aka gudanar a baya, a karo na farko, an sanya Tiktok cikin batutuwan da aka tattauna a shawarwarin na wannan zagaye. Yadda Sin da Amurka suka cimma daidaito a kan batun, ya kuma sake shaida cewa, samun moriyar juna shi ne tushen huldar kasashen biyu ta fannin tattalin arziki da cinikayya.

Hada karfi da karfe shi ne mafita daya tilo, a yanayin da ake ciki na karancin karfin bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Ba za a rasa samun sabanin ta fannin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka ba, amma duk da haka, akwai mafita idan sun dinga yin shawarwari da juna. A gaba, ya kamata sassan biyu su tabbatar da daidaito da shugabannin kasashen biyu suka cimma, musamman ma ya kamata Amurka ta samar da yanayin kasuwanci mai adalci ga kamfanonin kasar Sin, ciki har da Tiktok, kuma ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, don su kiyaye nasarorin da suka cimma a shawarwarin, don tabbatar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu yadda ya kamata. (Lubabatu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet