Aminiya:
2025-09-18@01:41:38 GMT

An dakatar da Max Air na tsawon wata 3 bayan hatsari a Kano

Published: 29th, January 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya, ta dakatar da zirga-zirgar jiragen Max Air na tsawon wata uku, bayan ɗaya daga cikin jiragen kamfanin, tayarsa ta yi bindiga yayin sauka a filin jirgin saman Malam Aminu Kano a daren ranar Talata.

Jirgin Max Air ƙirar Boeing 734 mai lamba 5N-MBD ne ya samu matsalar kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a Amurka Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Dukkanin fasinjoji 53 da ke cikin jirgin sun kuɓuta cikin ƙoshin lafiya.

Wannan shi ne karo na uku da jirgin Max Air ke fuskantar matsala cikin watanni uku da suka gabata.

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasa (NCAA), ta sanar da dakatarwar domin bai wa kamfanin damar sake duba yanayin aikinsa, yayin da Hukumar Binciken Haɗuran Jiragen Sama (NSIB), ta fara bincike kan lamarin.

Daraktan Harkokin Jama’a da Kare Haƙƙin Fasinjoji na NCAA, Michael Achimugu, ya yi ƙarin haske kan lamarin.

Ya ce, “Za mu iya gano musababbin wannan hatsari ne kawai bayan binciken NSIB, amma dole ne mu ɗauki matakan kariya don tabbatar da tsaro.”

Ya ƙara da cewa, “A lokacin dakatarwar watanni uku, NCAA za ta gudanar da cikakken bincike kan tsaro da kuma ƙarfin tattalin arziƙin Max Air.

­“Kamfanin jirgin zai iya ci gaba da zirga-zirga ne kawai idan ya cika dukkanin sharuɗan da ake buƙata.”

NCAA ta nemi afuwar fasinjojin da wannan mataki zai shafa, amma ta jaddada cewa lafiyar fasinjoji ita ce abin da yafi muhimmanci a wajenta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ababen fashewa dakatarwa fashewa Hatsari Jiragen sama Taya

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara