Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ci Gaba Da Tallafawa UNRWA Wajen Gudanar Da Ayyukanta
Published: 30th, January 2025 GMT
Yayin da dokar haramtawa hukumar kula da ‘yan gudun hijirar Palasdinu ta MDD (UNRWA) yin aiki a Isra’ila ke gab da fara aiki, kwamitin sulhu na majalisar ya kira wata budaddiyar muhawara dongane da batun, inda wakilin Sin da wakilan sauran kasashe suka sake bayyana goyon bayansu ga hukumar.
Wakilin Sin na dindindin a MDD Fu Cong, ya yi kira ga Isra’ila da ta daina dakatarwa da kai wa hukumar hari, kana ta dakatar da zartar da dokoki masu ruwa da tsaki, yana mai kira ga kasashen duniya su ci gaba da goyon bayan hukumar wajen gudanar da ayyukanta da marawa MDD da kwamitin sulhun baya, wajen daukar matakan gaggawa domin tabbatar da hukumar ta gudanar da ayyukanta.
A cewar Fu Cong, goyon bayan hukumar na da alaka da kiyaye ikon tsarin dokokin kasa da kasa da kuma huldar kasashe da bangarori daban-daban da kiyaye rayukan miliyoyin ‘yan Gaza da kwanciyar hankalin yankin yamma da kogin Jordan da kuma warware batun Palasdinu a siyasance.
Fu cong ya kuma nanata cewa MDD da kwamitin sulhu na da nauyin daukar matakai na gagagwa da suka dace, domin tabbatar da hukumar na gudanar da ayyukanta da kuma kare yunkurin kakaba matakin ladaftarwa na bai daya kan al’ummar Gaza. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA
Kwamitin koli na tsaron kasa ya amince da yarjejeniyar da hukumar makamashin nukiliya ta duniya IAEA
Kwamitin koli na tsaron kasar Iran ya yi gargadin cewa, idan aka dauki wani mataki na nuna adawa ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran da cibiyoyinta na makamashin nukiliya, ciki har da sake farfado da kudurorin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da suka kare, za a dakatar da aiwatar da tsare-tsare da yarjejeniyoyin da aka kulla da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA.
Sakatariyar kwamitin tsaron kasar Iran ta fitar da wata sanarwa a jiya Lahadi, bayan yarjejeniyar da aka rattabawa hannu tsakanin Seyyed Abbas Araqchi da Rafael Grossi. An yi wannan bayani ne dangane da tsare-tsare da ministan harkokin wajen kasar da babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA suka rattabawa hannu dangane da tsarin mu’amala tsakanin Iran da IAEA bisa la’akari da sabbin yanayi da ake ciki bayan hare-haren soji da gwamnatin yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan cibiyoyin makamashin nukiliya na kasar Iran bisa tsarin kariya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci