Kiristoci sun yi addu’ar ɗorewar zaman lafiya a Kudancin Kaduna
Published: 29th, January 2025 GMT
Ƙungiyar Shugabannin Kiristoci na Kudancin Kaduna (SKCLA) ta yi kira ga al’ummar yankin da su rungumi haɗin kai da ƙaunar juna a matsayin tubalin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.
Shugaban ƙungiyar SKCLA, Fasto Emmanuel Nuhu Kure ne ya yi wannan kiran ga mazauna yankin a wajen taron addu’ar shekara-shekara da ake gudanarwa a garin Kafanchan don kyautata alaƙarsu da Ubangiji tare neman ɗauki daga gare Shi don samun zaman lafiya da wadata.
“Lokaci ya yi da za mu haɗa kai da tunanin mu waje ɗaya da manufa ɗaya don sake gina al’ummomin Kudancin Kaduna,” inji Kure.
“Dole ne mu koyi son makwabtanmu musulmai ba tare da wariya ba. Idan har babu haɗin kai, ba za mu samu makoma mai kyau ba.”
Malamin ya jaddada buƙatar sake gina yankin inda ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da ta jiha kan inganta tsaro a yankin.
“A cikin shekaru biyu da suka gabata zamu iya cewa mun samu zaman lafiya, yanzu za mu iya numfasawa da kyau kuma mu yi barci idanunmu biyu a rufe, muna jin daɗin zaman lafiyar da ke gudana,” inji shi.
Kure ya kuma yi kira ga manyan mutane daga Kudancin Kaduna da su yi amfani da wannan damar na zaman lafiya wajen kafa masana’antu da za su samar da aikin yi ga matasan yankin ba tare da jiran gwamnati sai ta yi komai ba.
Babban baƙo mai jawabi, Bishop Zakka Nyam na Cocin Anglikan da ke Kano, ya bayyana fatansa na kasancewar shekara 2025 da ta zamo shekarar sauyi ga Kudancin Kaduna.
Ya ce lokaci ya yi da jama’ar yankin za su yi watsi da dabi’ar yawaita gine-ginen Otal a yankin maimakon haka su fara gina masana’antu don sarrafa abubuwan da ake nomawa a yankin.
A nasa jawabin, Mataimakin Kakakin Majalisar Dokoki na Jihar Kaduna, Hon. Henry Magaji Danjuma ya bayyana yankin Kudancin Kaduna a matsayin yanki mai yalwar albarkatu, tare da yin kira ga mazauna yankin da su mara wa gwamnatinsu baya don samun ƙarin romon dimokuraɗiyya.
An gudanar da addu’o’i da waƙe-waƙen ibada musamman don ceto yankin, da Jihar Kaduna da kuma ƙasar baki ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
A ranar 30 ga wata ne shugabannin kasashen Sin da Amurka suka gana da juna a birnin Busan na kasar Koriya ta Kudu, lamarin da ya jawo hankulan kasa da kasa, inda shugabannin 2 suka yi musayar ra’ayoyi dangane da huldar da ke tsakanin kasashen 2 da al’amuran da suka jawo hankulansu. Sun amince da inganta hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin tattalin arziki da cinikayya da makamashi da kyautata mu’amalar al’adu.
A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jaddada cewa, yana son hada kai da shugaba Donald Trump na Amurka wajen aza harsashi mai kyau na raya huldar da ke tsakanin kasashen 2, tare da samar wa juna kyakkyawan yanayin samun ci gaba. A nasa bangaren, shugaba Trump ya ce, kasar Sin, abokiyar Amurka ce mafi girma. Kasashen 2 za su hada kansu wajen samun nasarar gudanar da manyan ayyuka da dama a duniya. Nan gaba Amurka da Sin za su kara samun nasara a hadin gwiwarsu. Shugabannin 2 sun amince su rika yin mu’amala da juna. Shugaba Trump yana sa ran kai ziyara a kasar Sin a farkon shekara mai zuwa, ya kuma gayyaci shugaba Xi ya ziyarci Amurka.
Masharhanta sun yi nuni da cewa, ganawar shugabannin 2 ta sanya tagomashi kan kyautatuwar huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, ta kuma tsara manufar raya huldar kasashen 2 a nan gaba, tare da kwantar da hankulan kasashen duniya.
Abubuwan tarihi da kuma hakikanin abubuwa sun nuna cewa, wajibi ne Sin da Amurka su zama abokan juna. A wannan muhimmin lokaci, ganawar da shugabannin kasashen 2 suka yi ta sake tsara manufar kyautata da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2. Muddin kasashen 2 suka aiwatar da muhimman daidaito da shugabannin 2 suka cimma, da mutunta ruhin adalci, tare da martaba juna da samun moriyar juna, to, za a raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 ba tare da wata matsala ba, da kuma kara samar da kwanciyar hankali da tabbaci a duniya. (Tasallah Yuan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA