Aminiya:
2025-06-15@11:52:40 GMT

Kiristoci sun yi addu’ar ɗorewar zaman lafiya a Kudancin Kaduna

Published: 29th, January 2025 GMT

Ƙungiyar Shugabannin Kiristoci na Kudancin Kaduna (SKCLA) ta yi kira ga al’ummar yankin da su rungumi haɗin kai da ƙaunar juna a matsayin tubalin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.

Shugaban ƙungiyar SKCLA, Fasto Emmanuel Nuhu Kure ne ya yi wannan kiran ga mazauna yankin a wajen taron addu’ar shekara-shekara da ake gudanarwa a garin Kafanchan don kyautata alaƙarsu da Ubangiji tare neman ɗauki daga gare Shi don samun zaman lafiya da wadata.

DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata An kama gungun masu yi wa Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura

“Lokaci ya yi da za mu haɗa kai da tunanin mu waje ɗaya da manufa ɗaya don sake gina al’ummomin Kudancin Kaduna,” inji Kure.

“Dole ne mu koyi son makwabtanmu musulmai ba tare da wariya ba. Idan har babu haɗin kai, ba za mu samu makoma mai kyau ba.”

Malamin ya jaddada buƙatar sake gina yankin inda ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da ta jiha kan inganta tsaro a yankin.

“A cikin shekaru biyu da suka gabata zamu iya cewa mun samu zaman lafiya, yanzu za mu iya numfasawa da kyau kuma mu yi barci idanunmu biyu a rufe, muna jin daɗin zaman lafiyar da ke gudana,” inji shi.

Kure ya kuma yi kira ga manyan mutane daga Kudancin Kaduna da su yi amfani da wannan damar na zaman lafiya wajen kafa masana’antu da za su samar da aikin yi ga matasan yankin ba tare da jiran gwamnati sai ta yi komai ba.

Babban baƙo mai jawabi, Bishop Zakka Nyam na Cocin Anglikan da ke Kano, ya bayyana fatansa na kasancewar shekara 2025 da ta zamo shekarar sauyi ga Kudancin Kaduna.

Ya ce lokaci ya yi da jama’ar yankin za su yi watsi da dabi’ar yawaita gine-ginen Otal a yankin maimakon haka su fara gina masana’antu don sarrafa abubuwan da ake nomawa a yankin.

A nasa jawabin, Mataimakin Kakakin Majalisar Dokoki na Jihar Kaduna, Hon. Henry Magaji Danjuma ya bayyana yankin Kudancin Kaduna a matsayin yanki mai yalwar albarkatu, tare da yin kira ga mazauna yankin da su mara wa gwamnatinsu baya don samun ƙarin romon dimokuraɗiyya.

An gudanar da addu’o’i da waƙe-waƙen ibada musamman don ceto yankin, da Jihar Kaduna da kuma ƙasar baki ɗaya.

Taron addu’o’in da aka gudanar a Kudancin Kaduna

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India

Jirgin saman fasinja da ke kan hanyarsa ta zuwa Landan wanda ya yi hatsari a birnin Ahmedabad na Indiya a ranar Alhamis.

Mutum ɗaya ne ya tsira daga cikin mutane 242 da ke cikin jirgin, tare da fasa gine-ginen likitoci da iyalansu.

Wani ɗan jarida na AFP ya ga gawarwakin da aka zaƙulo daga wurin da jirgin ya faɗi, da kuma bayan jirgin ƙirar Boeing 787-8 Dreamliner a rataye a gefen wani gini da ya rutsa da shi a lokacin cin abinci.

Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari

“Iftila’in da ya afku a Ahmedabad ya ba mu mamaki da kuma ɓacin rai. Abin takaici ne da ba za a iya cewa komai ba,” in ji Firayim Minista Narendra Modi a bayaninsa bayan jirgin Air India mai lamba 171 ya yi hatsari bayan tashinsa.

Kwamishinan ’yan sandan birnin GS Malik ya ce gawarwakin fasinjoji da waɗanda abin ya rutsa da su a ƙasa na daga cikin 204 da aka gano zuwa yanzu, yayin da ma’aikatan lafiya ke jinya da dama waɗanda suka jikkata a birnin.

Yayin da aka fara fargabar mutuwar duk wanda ke cikin jirgin, jami’in kula da lafiya na jihar Dhananjay Dwivedi ya shaida wa AFP cewa “an tabbatar da wanda ya tsira” kuma ana jinyar shi a asibiti.

Ɗan jaridar na AFP ya ga wani gini ya ƙone ƙurmus bayan faɗuwar jirgin, inda hayaƙi ya turnuke sama da wani ɓangare na jirgin a ƙasa.

“Rabin jirgin ya faɗo cikin ginin mazaunin da likitoci ke zaune tare da iyalansu,” in ji Krishna, wani likita da bai bayyana cikakken sunansa ba.

Krishna ya ce ya ga “kusan gawarwaki 15 zuwa 20 da suka ƙone”, yayin da shi da abokan aikinsa suka ceto ɗalibai kusan 15.

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Indiya ta ce, akwai mutane 242 a cikin jirgin, ciki har da matuƙan jirgi biyu da ma’aikatan cikin jirgin 10.

Kamfanin jirgin Air India ya ce, akwai fasinjojin Indiya 169 da 53 ‘yan Burtaniya da ‘yan Portugal bakwai, da kuma wani ɗan ƙasar Kanada a cikin jirgin da zai nufi filin jirgin saman Gatwick na Landan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya