‘Yan Tawayen Sudan Sun Kona Wani Bangaren Matatar Mai Ta Al-Jili Da Ke Birnin Khartoum Bahri
Published: 28th, January 2025 GMT
Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Kungiyar Rapid Support Forces sun kai hari kan matatar mai ta Al-Jili da ke birnin Khartoum na kasar Sudan
Mayakan kungiyar dakarun kai daukin gaggawa sun kai hari kan matatar mai ta Al-Jili da ke birnin Khartoum Bahri, wadda ita ce matatar mai mafi girma a kasar Sudan, wadda take samar da man fetur a yawancin jihohin kasar ta Sudan, duk kuwa da cewa kwararru sun tabbatar da takaitar barnar da aka yi wa matatar Man duk da tashin bam da aka samu a cikin matata da ya tilasta dakatar da duk wani aiki a cikinsa.
Sojojin Sudan sun yi amfani da dama a lokacin da dakarun kungiyar Rapid Support Forces suke fita daga matatar man, zuwa shiyar lardin Darfur domin neman mafaka mafi aminci, inda sojojin suka yi musu luguden bama-bamai ta hanyar jiragen saman yaki, wasu rahotonni suna cewa; Har yanzu Dakarun kai daukin gaggawan ne suke iko da mafi yawan jihohin lardin Darfur da ke arewacin kasar ta Sudan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp