Qassem : Al’ummar Labanon Ba Za Su Manta Da Irin Goyon Bayan Da Iran Da Iraki Ta Yi Musu Ba
Published: 28th, January 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya ce al’ummar kasar Labanon ba za su manta da irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Iraki ta yi musu ba a lokacin da Isra’ila ke kai musu hare-hare.
Sheikh Naim Qassem ya bayyana hakan ne a wani jawabi da aka watsa kai tsaye a yammacin jiya Litinin.
“Nasarar Gaza ta al’ummar Falasdinu ce, da al’ummomin yankin da suka tallafa musu da kuma duk masu neman ‘yanci a fadin duniya.” Inji shi.
Sheikh Qassem ya jaddada cewa tsayin daka wani zabi ne na siyasa, kasa da kuma jin kai don fuskantar mamayar Isra’ila da ‘yantar da yankunan da ta mamaye.
Ya bayyana cewa an cimma manufofin da ke tattare da farmakin Operation Al-Aqsa wanda kungiyoyin gwagwarmaya na Gaza suka kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023.
Sheikh Qassem ya bayyana hare-haren da Isra’ila ke kai wa kan Lebanon da zirin Gaza a matsayin wani harin wuce gona da iri da Amurka da wasu gwamnatocin kasashen yammacin duniya ke goyon bayansu.
Ya ce, kungiyar Hizbullah ta tabbatar da cewa tana da hadin kai ta kuma cike gibin shugabanci cikin kankanin lokaci bayan kisan babban sakatarenta Sayyed Hassan Nasrallah a wani kazamin harin da Isra’ila ta kai a kudancin Beirut a karshen watan Satumba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
A ci gaba da hare-haren da dakarun Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza, yanzu adadin Falasdinawan da suka kashe ya kai 60,034.
A cewar wasu alkaluma daga Ma’aikatar Lafiya ta Gaza, baya ga wannan, adadin wadanda aka raunata kuma a yanzu sun haura 145,870.
Ma’aikatar ta kuma ce har yanzu ana zargin akwai mutanen kuma da ke karkashin baraguzan gine-ginen da aka rusa, wadanda ba za a iya ciro su daga ciki ba.
Fiye da kaso daya cikin uku na mutanen yankin na shafe kwanaki ba su ci abinci ba, kamar yadda wani rahoton samar da abinci mai lakabin IPC na Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar.
Rahoton ya ce ana samun karin hujjoji da ke nuna ana fama da yunwa da karancin abinci da kuma karuwar mace-mace masu alaka da yunwa a yankin da sama da mutum miliyan biyu da dubu dari daya ke rayuwa a cikinsa.
Hukumomi daban-daban na Majalisar Dinkin Duniya dai sun yi gargadin cewa ana fama da matsananciyar yunwar da aka kirkira da gangan a Gaza, inda a iya wannan watan, rahotanni suka tabbatar da mutuwar mutum 63, dalilin yunwar.
Hukumomin dai sun dora wa Isra’ila duk alhakin matsalolin, kasancewar ita ta yi wa yankin kawanya ta kuma hana a shigar da kayan agaji.
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya ce: “Abubuwa ne ga su nan a Zahiri, ba a boye suke ba. Falasdinawan da suke Gaza na cikin mawuyacin hali da tsananin bukatar agaji.
“Wannan ba wai gargadi muke yi ba. Gaskiya ce ga ta nan karara. Dole kayan agaji su ci gaba da kwarara. Abinci, ruwan sha, magunguna da man fetur dole su ci gaba da shiga ba tare da kowanne irin tarnaki ba,” in ji Guterres.