Qassem : Al’ummar Labanon Ba Za Su Manta Da Irin Goyon Bayan Da Iran Da Iraki Ta Yi Musu Ba
Published: 28th, January 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya ce al’ummar kasar Labanon ba za su manta da irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Iraki ta yi musu ba a lokacin da Isra’ila ke kai musu hare-hare.
Sheikh Naim Qassem ya bayyana hakan ne a wani jawabi da aka watsa kai tsaye a yammacin jiya Litinin.
“Nasarar Gaza ta al’ummar Falasdinu ce, da al’ummomin yankin da suka tallafa musu da kuma duk masu neman ‘yanci a fadin duniya.” Inji shi.
Sheikh Qassem ya jaddada cewa tsayin daka wani zabi ne na siyasa, kasa da kuma jin kai don fuskantar mamayar Isra’ila da ‘yantar da yankunan da ta mamaye.
Ya bayyana cewa an cimma manufofin da ke tattare da farmakin Operation Al-Aqsa wanda kungiyoyin gwagwarmaya na Gaza suka kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023.
Sheikh Qassem ya bayyana hare-haren da Isra’ila ke kai wa kan Lebanon da zirin Gaza a matsayin wani harin wuce gona da iri da Amurka da wasu gwamnatocin kasashen yammacin duniya ke goyon bayansu.
Ya ce, kungiyar Hizbullah ta tabbatar da cewa tana da hadin kai ta kuma cike gibin shugabanci cikin kankanin lokaci bayan kisan babban sakatarenta Sayyed Hassan Nasrallah a wani kazamin harin da Isra’ila ta kai a kudancin Beirut a karshen watan Satumba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
A wani bayani na hadin gwiwa da hukumar makamashin Nukiliya ta Iran da kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran su ka fitar, sun bayar da umarnin a bude wani wuri na daban na sirri domin ci gaba da tace sanadarin Urani’um, sannan kuma a maye gurbin bututu tace sanadarin mai mataki na daya, da mai mataki na shida a cibiyar “Pardo.”
Bayanin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sanarwar da ta fito daga kwamitin alkalai na hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa akan Iran.
Bugu da kari, bayanin na Iran ya kuma ce; A kodayaushe jamhuriyar musulunci ta Iran tana aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta, kuma har ya zuwa yanzu babu wani rahoto na hukumar wanda ya bayyana cewa; Iran ba ta aiki da ka’idojin hana yaduwar makaman Nukiliya.”
Haka nan kuma bayanin ya ambaci cewa; Tare da cewa Iran tana daukar rahoton da cewa na siyasa ne, wanda Amurka da kasashen turai suke amfani da hukumar a matsayin makami, ba tare da dogaro da wani dalili na ilimi ba.
Har ila yau Iran din ta zargi Amurka da kasashen na turai da wuce gona da iri wajen tsara rahoton da yake cin karo da rahoton da shugaban hukumar ta makamashin Nukiliya ya fitar, wanda bai sami wani abu mai shiga duhu ba a cikin Shirin na Iran na zama lafiya.