Aminiya:
2025-05-01@02:25:20 GMT

Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari

Published: 27th, January 2025 GMT

Tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya ce ya bayar da hayar ɗaya daga cikin gidaje uku kacal da ya mallaka domin sayen abinci.

Buhari ya faɗi hakan a yayin wani taro na jam’iyyar APC da aka gudanar ranar Litinin a Fadar Gwamnatin Katsina.

Tsohon Shugaban Ƙasar ya ce duk da ya shafe shekaru takwas a kan madafan iko, bai yi amfani da kujerar mulki wajen azurta kansa ba.

“Nijeriya ƙasa ce mai wuyar sha’ani ta fuskar jagoranci amma galibin ’yan ƙasar ba su fahimci hakan ba.

“Ba za a taɓa fahimtar irin sarƙaƙiyar da ke cikin riƙo da akalar jagoranci ba da ma ita kanta Ƙasa Nijeriya sai mutum ya tsinci kansa a kan madafan iko.

“A yanzu na ƙara kyan gani da lafiya fiye da yadda nake a lokacin ina Fadar Gwamnatin Nijeriya.

“Duk wanda ya ganni a yanzu zai ce na samu lafiya fiye da yadda nake a lokacin ina shugabancin Nijeriya.

“Duk da cewa na shafe shekaru takwas a matsayin Shugaban Ƙasa, amma gidaje uku kacal na mallaka — ɗaya a Daura, sai guda biyu a Kaduna.

“A yanzu na bayar da hayar ɗaya daga cikin gidajen da ke Kaduna ina samun kuɗin sayen abinci,” a cewar Buhari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kaduna Muhammadu Buhari

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna

A Kaduna, an kama wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, ciki har da wani da ya ce ya koma jihar ne domin kafa sabuwar ƙungiya bayan an kama abokan aikinsa a Kwara.

Haka kuma, an kama wasu biyu da ke ɗauke da bindigogi.

‘Yansanda sun gano makamai da dama, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 da AK-49, da kuma wasu makamai da aka ƙera a gida.

Wannan aiki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar garkuwa da mutane da safarar makamai a faɗin ƙasar.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ana ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu da zarar an kammala binciken.

Ya kuma yaba da goyon bayan da al’umma da jami’an tsaro suka bayar wajen nasarar kama su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi