An Watsa Bidiyon Dandanon Shagalin Murnar Bikin Bazara Na CMG A Karon Farko A Najeriya
Published: 28th, January 2025 GMT
A ranar 25 ga wata, agogon Najeriya, ofishin karamar jakadiya kasar Sin dake Legas, da tawagar Sinawa wadanda ke kasar, sun gudanar da jerin ayyuka don yin maraba da murnar bikin Bazara na shekarar maciji bisa kalandar gargajiyar Sinawa. An gudanar da bikin nune-nunen abinci, da nune-nunen kayayyaki, da liyafar maraba bi da bi, wanda ya samu halartar mutane sama da 2,000 da suka hada da Sinawa dake kasar da abokai ‘yan Najeriya.
Kafin an fara liyafar a maraice, an watsa bidiyon dandanon shagalin murnar bikin Bazara na shekarar maciji na babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG, Kyan hoton bidiyon mai kayatarwa kuma mai cike da ma’anar kimiyya da fasaha ya matukar burge bakin da ke wurin, ya kuma tada sha’awa mai karfi na yawancin baki ‘yan Najeriya, masu kallo sun kalli bidiyon a tsanake kuma sun yi kyakkyawar tafawa ma bidiyon. (Mohammed Yahaya)
এছাড়াও পড়ুন:
Fiye Da Mata 300 Ne Cikinsu Ya Zube Saboda Rashin Abinci Mai Gina Jiki A Gaza
Ofishin watsa labaru na hukuma a Gaza ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da kuma kungiyoyin jin kai, da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu na doka da kyawawan halaye, su tsoma baki domin ceto da fararen hula a Gaza.
Ofishin watsa labarun na hukuma a Gaza ya kuma yi kira da a tseratar da mutanen na Gaza daga yunuwar da suke fuskanta, ta hanyar yin matsin lamba da a bude hanyoyin shigar da kayan taimako da agaji cikin yankin.
Ita kuwa hukumar lafiya ta yanki ta sanar da yadda sojojin na HKI suke ci gaba da kai hare-hare akan asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya da hakan ya sabawa dokokin yaki.
Ofishin watsa labaru na hukumar Gaza ya kuma sanar da cewa; Har yanzu yankin yana fama da matsanancin killace shi da aka yi, da hana shigar da kayan agaji.
Daga lokacin sake komawa yaki na bayan nan da HKI ta yi, tun kwanaki 80 da su ka gabata,mutane 58 sun rasa rayukansu saboda rashin abinci mai gina jiki, sai kuma wasu 242 da yunuwa da rashin magani su ka kashe,mafi yawancinsu wadanda su ka mayanta. Haka nan kuma wasu mata masu ciki fiye da 300 su ke cikin nasu ya zube saboda rashin abinci mai gina jiki.