Aminiya:
2025-06-15@01:53:13 GMT

’Yan sanda sun yi ƙarin haske kan barazanar harin ’yan ta’adda a Kano

Published: 27th, January 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta yi ƙarin haske dangane da barazanar harin ’yan ta’adda da ta yi gargaɗin aukuwarsa a bayan nan.

Da yake yi wa manema labarai jawabi, Kwamishinan ’Yan sandan Kano, Salman Dogo Garba, ya ce sun ɗauki matakan da suka dace biyo bayan barazanar harin ’yan ta’adda musamman a yayin taron Maulidin Shehu Ibrahim Inyass na ƙasa da aka gudanar ranar Asabar a jihar.

Ɗan shekara 30 ya mutu a kududdufi a Kano ’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —Bincike

“Mun ankarar da jama’a sannan muka ɗauki matakan da suka dace domin tunkarar lamarin,” in ji CP Garba.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin waɗanda ake zargin dangane da lamarin sun tsere daga jihar a sakamakon bayanan sirri da rundunar ta tattara.

“Mun kuma samu nasarar cafke wani mutum guda da ya shigo Kano ya samu mafaka a wani coci.

“Haka kuma mun samu ababen fashewa da sauran kayayyakin da aka yi yunƙurin kai harin da su,” a cewar CP Garba.

Kwamishinan ya jaddada muhimmancin tattara bayanan sirri domin daƙile duk wata barazana da ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da tsaro.

CP Garba ya kuma yi tsokaci irin ƙalubalen da suke fuskanta dangane da yadda ake siyasantar da duk wani lamari musamman a wurare irin Jihar Kano, sai dai ya nanata cewa za su ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da kiyaye da doka da oda.

“Komai sai an siyasantar da shi a Jihar Kano hatta abincin da muke ci. Sai dai ina ƙara tabbatar da cewa rundunar ’yan sandan da nake jagoranta ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da tsaro a jihar nan.

“Tun daga kan iyaye da kakanni nake cikin ɗariƙar Tijjaniyya saboda haka ba zan gushe ba wajen zama jakada na zaman lafiya da tabbatar da tsaro ba.

Kwamishinan ya ƙara tabbatar wa al’ummar jihar cewa rundunar ’yan sandan za ta ci gaba faɗi tashin domin daƙile duk wata barazana da za ta kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron jihar.

Ya buƙaci al’umma da suka kasance masu lura da sanya ido domin bai wa hukumomin tsaro haɗin kai na tabbatar da tsaro a jihar.

Ya kuma miƙa godiya ga duk waɗanda suke bai wa jami’an tsaro goyon baya na wanzar da aminci a jihar.

A bayan nan ne dai aka zargi rundunar ’yan sandan jihar da yunƙurin hana gudanar da Maulidin Shehu Inyass na ƙasa bayan gargaɗin da ta yi kan barazanar harin ’yan ta’adda a jihar.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan ta adda Jihar Kano tabbatar da tsaro barazanar harin yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran

Farashin Man Fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin da Isra’ila ta kai wa Iran, lamarin da ya tayar da hankalin masu zuba jari.

Ana fargabar cewa rikicin da ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin ƙasashen biyu zai iya kawo tangarɗa wajen samar da man fetur daga yankin Gabas ta Tsakiya.

An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8

Wani muhimmin wurin da ake safarar man fetur na duniya, wato mashigar Hormuz da ke kusa da Iran na da matuƙar tasiri, domin kashi ɗaya cikin biyar na dukkanin man da ake fitarwa daga nan ne ake bi da shi.

Amma duk da haka, kasuwannin hannun jari sun fuskanci faɗuwar daraja saboda rashin tabbas da harin ya haifar.

Sai dai darajar wasu hajojin da ake ɗauka amintattu a lokutan rikicin irin su zinariya da kuɗin ƙasar Japan, Yen sun tashi sama, domin masu zuba jari na ƙoƙarin neman mafaka a cikinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas