Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@14:35:00 GMT

An Yabawa Darikar Tijjaniyya akan Samar da Hadin kai a Najeriya.

Published: 27th, January 2025 GMT

An Yabawa Darikar Tijjaniyya akan Samar da Hadin kai a Najeriya.

Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima, ya yaba da irin gudunmawar da darikar Tijjaniyya ke bayarwa wajen samar da hadin kai a tsakanin al’ummar musulmin kasar nan.

 

Mataimakin shugaban kasar ya yi wannan yabon ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron Mauludin bana 2025 na marigayi Sheikh Ibrahim Nyass, jagoran darikar Tijjaniyya a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.

 

Mataimakin wanda ya samu wakilcin Alhaji Babagana Fannami, Ya yabawa kungiyar musulmi bisa tsayin daka a tsawon karnukan da suka gabata akan koyarwar addinin musulunci na gaskiya.

 

Shettima wanda shi ne babban bako na musamman a wajen taron, ya yaba da tsarin jagoranci na darikar ‘Sufi’ ga bil’adama.

 

Babban bako na musamman ya jaddada irin tsayin dakan da darikar Tijjaniyya ke da shi wajen koyi da darussan rayuwan Annabi Muhammad ba tare da tauye lamuran fikihu na Musulunci ba.

 

Don haka ya tunatar da musulmi da su yi koyi da koyarwa ta gaskiya ta Musulunci, su guje wa tsatsauran ra’ayi.

 

Hakazalika babban mai masaukin baki Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yaba da kokarin Darikar Tijjaniyya wajen wanzar da zaman lafiya da zumunci da sauran kungiyoyin a Najeriya.

 

“A matsayina na mai masaukin baki, dole ne mu yaba muku da kuka zo Kano daga nesa da kusa domin halartar mauludin bana na Sheik Ibrahim Nyass.”

 

Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Khalifa Dr. Muhammadu Sanusi II, ya yi addu’ar samun hadin kan musulmin duniya baki daya da kuma hakuri da sauran mabiya addinai.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro Tijaniyya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi.

Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan dake baiyana cewa rashin aikin yi ya karu a najeriya da kaso 5.3 a farkon wannan shekarar, kazalika binciken ya baiyana cewa wadanda basu yi karatu mai zurfi ba sun fi wadanda suka yi karatu mai zurfi samun aikin yi.

NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya

Wadansu dalilai ne ke kara kawo rashin aikin yi a Najeriya?
Wadansu hanyoyi za’a bi wajen magance rashin aikin yi?
Wadannan da ma wasu tambayoyi na cikin batutuwan da Shirin Najeriya A Yau zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya