An Yabawa Darikar Tijjaniyya akan Samar da Hadin kai a Najeriya.
Published: 27th, January 2025 GMT
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima, ya yaba da irin gudunmawar da darikar Tijjaniyya ke bayarwa wajen samar da hadin kai a tsakanin al’ummar musulmin kasar nan.
Mataimakin shugaban kasar ya yi wannan yabon ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron Mauludin bana 2025 na marigayi Sheikh Ibrahim Nyass, jagoran darikar Tijjaniyya a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.
Mataimakin wanda ya samu wakilcin Alhaji Babagana Fannami, Ya yabawa kungiyar musulmi bisa tsayin daka a tsawon karnukan da suka gabata akan koyarwar addinin musulunci na gaskiya.
Shettima wanda shi ne babban bako na musamman a wajen taron, ya yaba da tsarin jagoranci na darikar ‘Sufi’ ga bil’adama.
Babban bako na musamman ya jaddada irin tsayin dakan da darikar Tijjaniyya ke da shi wajen koyi da darussan rayuwan Annabi Muhammad ba tare da tauye lamuran fikihu na Musulunci ba.
Don haka ya tunatar da musulmi da su yi koyi da koyarwa ta gaskiya ta Musulunci, su guje wa tsatsauran ra’ayi.
Hakazalika babban mai masaukin baki Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yaba da kokarin Darikar Tijjaniyya wajen wanzar da zaman lafiya da zumunci da sauran kungiyoyin a Najeriya.
“A matsayina na mai masaukin baki, dole ne mu yaba muku da kuka zo Kano daga nesa da kusa domin halartar mauludin bana na Sheik Ibrahim Nyass.”
Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Khalifa Dr. Muhammadu Sanusi II, ya yi addu’ar samun hadin kan musulmin duniya baki daya da kuma hakuri da sauran mabiya addinai.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
Gwamnatin Nijeriya ta ayyana gobe Alhamis 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar albarkacin bikin murnar Ranar Ma’aikata ta Duniya.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo, ya fitar a yammacin wannan Larabar.
AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsuSanarwar ta ambato ministan yana yaba wa ma’aikatan ƙasar kan sadaukarwa da jajircewar da suke yi wajen gudanar da ayyukansu.
Ministan ya kuma yaba musu kan gudunmawar da suke bayarwa wajen ciyar da Nijeriya gaba.
Ana dai gudanar da bikin Ranar Ma’aikata a ranar 1 ga watan Mayun kowace shekara a sassan duniya.