Ana zargin ’yan Majalisar Dokoki ta Ƙasa sun ɓullo da sabon salon cin hanci inda suke tatsar jami’o’i da sauran manyan cibiyoyin ilimi na tarayya.

Kafar yaɗa labarai ta Premium Times ta ruwaito cewa ’yan majalisar suna barazana ga kowane shugaban jami’a ya ba su cin hancin Naira miliyan takwas kafin sun amince da kasafin makarantarsa na shekarar 2025.

Binciken ya gano cewa kwamitin manyan makarantu da na Asusun Tallafin Manyan Makarantu (TETFUND) a Majalisar Wakilai da ta Dattawa sun buƙaci kuɗaɗen ne daga shugabannin manyan makarantun kafin su amince da kasafinsu na 2025.

’Yan majalisar sun nemi kowanne daga cikin shugaban Jami’o’in Tarayya 60 da ke ƙasar nan ya ba su Naira miliyan huɗu ga kwamitin majalisar dattawa da kuma Naira huɗu ga kwamitin majalisar wakilai kafin su amince da kasafin makarantarsa.

Boko Haram ta kashe sojoji 22 da mayaƙan JTF a Borno NAJERIYA A YAU: Dabarun Bunƙasa Kasuwanci Ta Intanet

’Yan majalisar na sa ran samun cin hancin jimillar Naira miliyan 480 daga wannan tsari. An kuma gano cewa sun sanya shuagabannin jami’o’i biyu daga yankin Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Yamma su tsara karɓar kuɗaɗen domin kauce wa tonon asiri.

Sun kuma yi barazanar ɗaukar mataki kan masu kunnen kashi a cikin shugabannin jami’an.

A halin yanzu kwamitocin majalisar dokoki ta kasa na bibiyar kasafin hukumomi da ma’aikatu da cibiyoyin gwamnati domin kare abin da suka gabatar a kasafin shekarar 2025 wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa babban zauren Majalisar a watan Oktoban 2024.

An jima dai ana zargin ’yan majalisa da neman na-goro da kuma cushe a kasafin kuɗi, inda suke barazanar bincike ga waɗanda suke ƙi su taka rawarsu.

Babu rufa-rufa

Shugabannin jami’o da suka bayyana a gaban kwamitocin domin kare kasafinsu sun zargi mambobin kwamitin da neman na-goro kafin su amince da kasafin.

Wasu daga cikin shugabannin jami’o’in da suka nuna turjiya kuma ana musu barazana da bincike ko ƙin amincewa da kasafin makarantunsu.

Bincike ya gano cewa shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai, Honorabul Hassan Fulata daga Jihar Jigawa ya ƙaddamar da karɓar na-goron ne daga ranar 16 ga watan Janairu a yayin wani zama da aka yi da wasu daga cikin shugabannin jami’o’in, inda aka gaya musu ƙarara abin da ake buƙata daga gare su.

Da farko an shirya fara zaman ne da misalin ƙarfe 10 na safe a,ma aka ɗage shi zuwa 3 na yamma saboda wasu shirye-shiryen bayan fage. Ɗaya daga cikin shugabannin jami’o’in da suka halarci zaman ya ce ’yan majalisar ba su yi wata rufa-rufa ba wajen bayyana abin da suke so.

Shugaban jami’ar wanda ya nemi a ɓoye sunansa saboda gudun zagon ƙasa, ya ce ’yan majalisar sun soke su saboda ƙin ba da haɗin kai kamar yadda sauran shugabannin manyan makarantu suka yi ba tare da wata turjiya ba. Ya ce da ta kai ’yan majalisar na musu barazana.

Wasu majiyoyi da suka halarci zaman sun ce mambobin kwamitin sun rika yi wa shugabannin jami’o’in shaguɓe, “da barazanar bincike idan ba mu yi musu abin da suke so ba,” kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Ya bayyana cewa yawancin hukumomi da cibiyoyin gwamnati na guna-guni kan wannan lamari kamar yadda shugabanni jami’o’i ke yi.

Yawancin shugabannin jami’o’i na kokawa bisa yadda ’yan majalisar ke yawan tatsar su kuɗaɗe, lamarin da yanzu ya ɗauki sabon salo saboda barazanar da ’yan majalisar ke musu da sunan bincike.

Wani shugaban jami’a ya bayyana damuwa game da yiwuwar a tura hukumar ICPC ta bincike su, kamar yadda aka yi a baya lokacin da binciken Premium Times ya bankaɗo irin wannan lamari na neman na-goro daga ’yan majalisar dokoki ta ƙasa.

A 2023 Premium Times ta bankaɗo yadda kwamitin manyan makarantu na majalisar wakilai ya ɓullo da salon tatsar kuɗaɗe daga jami’o’i da kwalejojin ilimi da kwalejojin kimiyya da ƙere-ƙere.

Rahoton ya fallasa yadda ’yan majalisar suka riƙa amfani da kamfanonin canjin kuɗaɗe domin karɓar kuɗaɗen haramun ɗin.

A ƙarshe badaƙalar ta kai ga bincike daga hukumar Yaƙi da Ci. Hanci (ICPC) amma kamar an shuka dusa.

Babu abin ICPC za ta yi?

Da yake magana game da ICPC, daya daga cikin ’yan majalisar ya sanae a wurin taron cewa, “Daga ICPC zuwa Shugaban ’Yan Sanda babu wanda ba ya bayyana a gabanmu domin kare kasafin kuɗinsu.”

Premium Times ta tuntuɓi kakakin ICPC, Demola Bakare, ta waya gane da batun ɗan Majalisar na cewa  to hukumar taba ba da kai bori ya hau. Amma ya yi dariya sannan ya yi watsi da zargin cewa hukumar na ba da cin hanci ga wani kwamiti.

“Har kun ban dariya, a wurinku na fara jin wannan maganar, amma zan bincika in ji” a cewar Mista Bakare wanda ya yi alƙawarin bayyana matsayin hukumar a gwamnatance daga bisani, amma bai yi hakan ba.

Ɓatar da sawu

Binciken ya gano cewa ’yan kwamitin sun wakilta wani jami’insu ya kula da tura kuɗaɗen ta asusan banki da yawa ta yadda ba za a iya bibiyar su ba. Wannan dabara da sa binciken Premium Times bai iya gano tafiyar kuɗaɗen ba, ko shin shugabannin jami’o’i sun ba da kai bori ya hau.

Binciken ya gano cewa amfani da asusun ajiya da yawa da ba kai tsaye ba da kuma wakilai na rage yiwuwar tura kuɗi zuwa wani asusun ajiya.

Turjiya

Da alama dai a wannan karon shugabannin jami’o’i da dama ba su da niyyar bin wannan umarni, inda suke nuna damuwa bisa yadda ’yan majalisa ke yawan tatsar kuɗaɗe daga hannunsu.

A lokuta da dama shugabannin manyan makarantun kan bayyana a gaban kwamitoci daban-daban na wucin gadi da an dindindin na Majalisar Wakilai da na Majalisar Dattawa kan dalillai daban-daban.

A ranar Laraba suka yi irin wannan zama da kwamitin majalisar dattawa amma tattaunawar ba ta yi zafi kamar na Majalisar Wakilai ba.

Ana iya tuna cewa a bara Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ’yan majalisar sun nemi cin hancin Naira miliyan biyar daga kowane shugaban jami’a kafin su amince da kasafin makarantarsa.

Da alama ƙarin kuɗin zuwa miliyan takwas a bana ya ƙara musu damuwa.

Bi-ta-da-ƙulli

Da alama ’yan majalisar sun mayar da Shugaban Jami’ar Tarayya ta Gusau, Farfesa Mu’azu Gusau, hadafinsu, inda yayin zaman nasu ma ranar 16 ga Janairu suka bayyana cewa za su “koya masa darasi saboda taurin kansa.”

Mahalarta taron sun bayyana cewa ’yan majalisar sun soki Farfesa Gusau saboda ya ki ba su haɗin kai kamar sauran shugabannin jami’o’i.

“Ba a san takamaiman abin ya yi musu ba da suka kafa masa ƙahon zuƙa, amma da alama ya ƙi amincewa ne da buƙatarsu ne.

“Wataƙila a baya ma ya yi watsi da buƙatarau, saboda su a kodayaushe kuɗi suke nema,” in ji majiyar da ta nemi a ɓoye sunanta.

’Yan majalisar ba su bayyana yadda za su ɗauki mataki a kansa ba, amma suna da tarihin amfani da barazana da kuma bincike domin tanƙwara mutane su yi yadda suke so.

Cinikin na-goro

A lokuta da dama da ake zargi kwamitoci sun shirya bincike da nufin tozarta wasu mutane, a dabarar su ta tursasa cibiyoyin gwamnati su taka rawar kiɗansu.

Zaman sirri na daga cikin dabarun da suke amfani da su domin tattaunawa da tursasa wa cibiyoyi sa hukumomin gwamnati kan cin hancin da za su ba su.

Kwamitin Majalisar Wakilai kan Manyan Makarantu na da tarihin hana ’yan jarida halartar zaman su, wanda hakan ke ba da damar yin ƙumbiya-ƙumbiya.

An nemi jin ta bakin Shugaban Kwamitin Majalisar Tarayya kan Ilimin Jama’a, Honorabul Hassan Fulata, domin jin martaninsa, amma har zuwa lokacin da aka kammala wannan labarin bai amsa kiran waya ko rubutaccen sakon da aka aika masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan majalisa a Majalisar Wakilai kwamitin majalisar yan majalisar sun Yan majalisar sun yan Majalisar Naira miliyan ya gano cewa na majalisar na Majalisar kamar yadda

এছাড়াও পড়ুন:

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

A zantawar Sule Lamido da BBC, ya bayyana cewa; an yi masa kora da hali a hedikwatar jam’iyyar ta PDP.

Ya kara da cewa, ya je hedikwatar jam’iyyar PDP ne; domin karbar fom na takarar shugabancin PDP, sai ya samu ofishin da ya kamata ya karba a kulle, da ya tambaya sai aka ce da shi, a hannun gwamnan Adamawa kadai zai samu fom din.

Lamido ya ci gaba da cewa, ba ya fata a kai ga matakin da za a hana shi shiga takarar, “domin ina tunanin rigimar cikin gida ce, sannan kuma za mu iya samun maslaha a cikin gidan. Amma idan hakan bai yiwu ba, daga nan kuma na san me zan yi,” in ji shi.

Haka zalika, Sule Lamido ya ce; a shirye yake ya tsaya takarar shugabancin jam’iyyar a zaben da za a yi lokacin babban taron jam’iyyar a watan Nuwamban wannan shekara a birnin Ibadan na Jihar Oyo.

Bugu da kari, Lamidon ya sha alwashin tafiya kotu idan har aka ki sayar masa da fom din tsayawa takarar.

Kazalika, rahotanni sun tabbatar da cewa; tuni tsohon ministan ayyuka na musamman, Kabiru Tanimu Turaki ya yanki nasa fom din, a daidai lokacin da aka ki sayar wa da tsohon gwamnan na Jigawa fom din takarar shugabancin jam’iyyar ta hamayya, wato PDP.

Har wa yau, Jam’iyyar PDP ta sanar da dage tantance dan takara daga ranar Talata zuwa wani lokaci nan gaba, duk da cewa; jam’iyyar ba ta fadi dalilin yin hakan ba.

Haka nan, sanar da Kabiru Tanimu Turaki a matsayin dantakarar maslaha daga Arewacin Nijeriya ya bar baya da kura, inda wasu daga cikin shugabannin jam’iyyar PDP na shiyyar Arewa maso yammacin kasar, shiyyar da Turaki ya fito suka yi watsi da matakin da gwamnoni suka dauka.

Kazalika, shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Sakkwato, Muhammad Bello Aliyu na cikin shugabannin da suka yi fatali da matakin da gwamnonin suka dauka, saboda a cewarsa, ba a ba su damar zama su tattauna ba, gabannin tsayar da Turakin. Kana kuma, an sake samun wasu jiga-jigan jam’iyyar daga Jihar Kebbi da suka yi fatali da wannan maslahar.

Dangane da wanan sabuwar rigima ko rikici, malami a kwalejin ilimi ta share fagen shiga jami’a da ke Kano kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Dakta Kabiru Sa’id Sufi ya ce; ana neman fama karaya ne a yunkurin gyara targade.

“Mun dauka cewa, tunda aka zo batun zaben shugabanci, matsalolin da jam’iyyar ke ciki sun kusa zuwa karse, musammman ganin har an yi kokarin rarraba mukamai zuwa shiyya-shiyya, amma kuma sai hakan ya bar baya da kura.

“Yanzu haka, an fara samun korafi daga bangarori da dama, ciki har da daga wadanda ake ganin ba su da wata matsala.”

Haka nan, ya kara da ce; hana Sule Lamido sayen fom din takarar shugabancin jam’iyyar, wani babban al’amari ne, domin kuwa a cewar tasa; hakan ya kara haifar da rashin gamsuwa a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

Ya ce, “Akwai da ma wasu da suke ganin an lasa musu zuma a baki a Arewacin kasar na tsayawa takara, sai daga baya suka gane cewa, ba da gaske ake ba. Idan aka duba, za a ga akwai rashin gamsuwa daga bangarori da yawa. Ko bangaren Shekarau ma, sun nuna rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da al’amuran.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta October 31, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi? October 31, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP