Rundunar Sojin Najeriya ta 8 da ke Sokoto ta bayyana ayyukanta na zamantakewar jama’a na yammacin Afirka WASA, a matsayin muhimmin kayan aiki don wanzar da hadin kai da ci gaba a yankin yammacin Afirka.

 

Babban Kwamandan Rundunar, Manjo Janar Ibikunle Ajose ya bayyana haka a wajen taron na bana da aka gudanar a Bataliya ta 26 dake jihar Sokoto.

 

Ajose ya ce hukumar ta WASA tana baiwa hafsoshi da sojoji da iyalansu damar yin mu’amala cikin yanayi mai kyau.

 

Ya bayyana cewa, tarihin wannan biki ya samo asali ne tun a shekarar 1901, a lokacin shigar da Najeriya cikin rundunar sojojin kasashen yammacin Afrika, saboda al’adu daban-daban na sojojin kasashen yammacin Afirka, shi yasa mahukunta a wancan lokaci suka gabatar da WASA duk shekara domin sojoji su shiga.

 

Kwamandan ya yi nuni da cewa zaman lafiya da hadin kai da ake samu a cikin sojojin Najeriya sakamakon manufofin WASA ne a yankin yammacin Afirka.

 

Manjo Janar Ibikunle Ajose ya kuma duba irin nasarorin da rundunar ta samu kan yaki da ‘yan bindiga da sauran tashe-tashen hankula da ke faruwa a yankin Arewa maso Yamma .

 

Ya ce, a shekarar 2024, rundunar ta samu nasarar gudanar da ayyukanta na yaki da ayyukan bata gari a duk fadin Nijeriya.

 

Ya ce nasarorin da aka samu sun hada da kaddamar da runduna ta 248 ta Recce a Illelah, da tura babban hafsan soji na musamman na Bataliya ta 7 a karamar hukumar Gudu a jihar Sokoto da kaddamar da sabbin kayan aiki na sojojin sama da sauran makaman yaki a Sokoto.

 

A cewarsa, abubuwan da suka faru sun haifar da nasarori da dama a ayyukan sojoji na fadin yanki na 8.

 

A nasa jawabin, gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin sana’o’i da tsaro, Kanar Ahmed Usman mai ritaya, ya yabawa kokarin rundunar na ci gaba da kulla alaka mai karfi da al’adunsu.

 

Aliyu ya ce bikin ya zama abin tunatarwa ne kan alhakin da ya rataya a wuyansu na bunkasa fahimtar juna, mutunta juna, da hadin kai a tsakanin kungiyoyi da al’ummomi daban-daban a yammacin Afirka.

 

NASIR MALALI/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wasa yammacin Afirka

এছাড়াও পড়ুন:

Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027

’Yan siyasar yankin Arewa na ganin dole sai da goyon bayansu ɗan takara zai yi nasara a zaben Shugaban ƙasa.

Hakan na zuwa ne bayan tsohon maitaimaka wa shugaban ƙasa a fannin siyasa, Alhaji Hakeem Baba-Ahmed ya yi wata hira, inda yake cewa, nan da wata shida yankin zai fitar da matsayarsa.

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC

Duk da cewa Hakeem ba shi ne mai magana da yawun al’ummar yankin ba, amma ana kallon sa a matsayin daya daga cikin manya a yankin, saboda tsohon matsayinsa na mai magana da yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF).

Tsarin siyasar kasar nan ya sa dole ne kowane dan takara ya zaga kowane lungu da sako na kasar nan kafin ya iya samun kuri’un da yake bukata don ya samu nasara.

Masana harkokin siyasa na ganin kalaman na Hakeem da ire-irensa na kan hanya, amma idan aka cika sharadi daya kacal.

“Rawar da Arewa za ta taka a zaben 2027 ba ta da wani bambanci da wadda ta saba takawa, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan ta ci gaba da zama dunkulalliya, mai alkibla daya,” in ji Malam Kabiru Sufi na Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a ta Jihar Kano.

Idan dai aka cika wannan sharaɗi, to duk wani ɗan takara ko datn Arewa ne sai ya nemi goyon bayan ‘yan Arewacin kafin ya yi nasara.

Ya bayar da misalin haɗakar da jam’iyyun siyasa suka yi kafin babban zaben 2015, inda jam’iyyun CPC da ACN da ANPP da wani ɓangare na APGA da wasu gwamnonin PDP suka kafa APC mai mulkin.

“Idan aka samu rarrabuwar kai kuma, to Arewa za ta zama kamar wani taron tsintsiya ne ba shara. Babu rawar da za ta taka”, in ji Sufi.

Malam Sufi ya ce ɗaya daga cikin dalilan da suka sa ‘yan Arewa ke jin cewa sai da su za a ci zaɓe shi ne yawan al’umma.

A zaɓen 2023 da ya gabata, sahihan kuri’un da ‘yan takara huɗun farko suka samu a jihohin Arewa sun zarta na Kudu da kusan miliyan biyar.

Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC da Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Mista Peter Obi na LP da Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na NNPP, sun samu jimillar kuri’u miliyan 13,716,667 a jihohin Arewa. Sun samu jimillar 9,020,741 a jihohin Kudu.

Bola Tinubu da ya lashe zaɓen ya samu jimillar 5,346,404 a jihohin Arewa, yayin da ya samu 3,206,969 a jihohin Kudu.

“In dai Arewa ta sake yin abin da ta yi a 2015, tabbas dole ne sai an nemi goyon bayanta, amma idan aka samu rarrabuwar kai za ta zama mushen gizaka – ana yi mata kallon za ta iya, amma kuma ba za ta iya ba,” kamar yadda Sufi ya bayyana.

Shin ko Arewan za ta iya magana da murya ɗaya?

Farfesa Abubakar Ma’azu, masanin harkokin siyasa ne a Jami’ar Maiduguri yana ganin za ta iya yin hakan.

“Idan aka duba, wadanda suka kafa Jam’iyyar APC sun fara yunkurin ne tun a 2011.

“Abin bai yiwu ba, amma suka shiga zabe a haka kuma suka sha kaye. Sai daga baya suka gano kuskurensu kuma suka yi nasara a 2015 bayan cim ma hadakar,” in ji shi.

Ko zai yiwu a iya cin zabe da kuri’un Arewa kawai? Kamar yadda ’yan Arewa ke tutiya da cewa sai da goyon bayansu za a ci zaɓen Shugaban ƙasa, haka ma sai dan takara ya samu kuri’u a Kudanci kafin ya yi nasara.

Kafin hadakar APC ta kayar da PDP mai mulki, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi takara har sau uku ba tare da nasara ba, har sai bayan da ya samu goyon bayan wasu jam’iyyu daga Kudu.

Buhari ya fara yin takara ce a Jam’iyyar APP a 2003, ya sake yi a 2007 a jam’iyyar bayan ta zama ANPP, sai a 2011 kuma ya yi a CPC.

Ana ganin shigar Jam’iyyar ACN ta Bola Tinubu cikin haɗakar APC ce ƙashin bayan nasarar Buhari, saboda yadda take da tasiri a jihohin Kudu maso Yamma da Yarabawa ke da rinjaye.

Kazalika, Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 ya samu kuri’u mafiya yawa a Arewaci (4,834,767) sama da kudanci (1,751,047), amma duk da haka bai yi nasara ba.

“Dole ne sai ɗan takara ya karaɗe ƙasa baki ɗaya, ya samu kuri’u a Kudu da Arewa kafin ya samu kowace irin nasara,” in ji Farfesa Ma’azu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya