Rundunar Sojin Najeriya ta 8 da ke Sokoto ta bayyana ayyukanta na zamantakewar jama’a na yammacin Afirka WASA, a matsayin muhimmin kayan aiki don wanzar da hadin kai da ci gaba a yankin yammacin Afirka.

 

Babban Kwamandan Rundunar, Manjo Janar Ibikunle Ajose ya bayyana haka a wajen taron na bana da aka gudanar a Bataliya ta 26 dake jihar Sokoto.

 

Ajose ya ce hukumar ta WASA tana baiwa hafsoshi da sojoji da iyalansu damar yin mu’amala cikin yanayi mai kyau.

 

Ya bayyana cewa, tarihin wannan biki ya samo asali ne tun a shekarar 1901, a lokacin shigar da Najeriya cikin rundunar sojojin kasashen yammacin Afrika, saboda al’adu daban-daban na sojojin kasashen yammacin Afirka, shi yasa mahukunta a wancan lokaci suka gabatar da WASA duk shekara domin sojoji su shiga.

 

Kwamandan ya yi nuni da cewa zaman lafiya da hadin kai da ake samu a cikin sojojin Najeriya sakamakon manufofin WASA ne a yankin yammacin Afirka.

 

Manjo Janar Ibikunle Ajose ya kuma duba irin nasarorin da rundunar ta samu kan yaki da ‘yan bindiga da sauran tashe-tashen hankula da ke faruwa a yankin Arewa maso Yamma .

 

Ya ce, a shekarar 2024, rundunar ta samu nasarar gudanar da ayyukanta na yaki da ayyukan bata gari a duk fadin Nijeriya.

 

Ya ce nasarorin da aka samu sun hada da kaddamar da runduna ta 248 ta Recce a Illelah, da tura babban hafsan soji na musamman na Bataliya ta 7 a karamar hukumar Gudu a jihar Sokoto da kaddamar da sabbin kayan aiki na sojojin sama da sauran makaman yaki a Sokoto.

 

A cewarsa, abubuwan da suka faru sun haifar da nasarori da dama a ayyukan sojoji na fadin yanki na 8.

 

A nasa jawabin, gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin sana’o’i da tsaro, Kanar Ahmed Usman mai ritaya, ya yabawa kokarin rundunar na ci gaba da kulla alaka mai karfi da al’adunsu.

 

Aliyu ya ce bikin ya zama abin tunatarwa ne kan alhakin da ya rataya a wuyansu na bunkasa fahimtar juna, mutunta juna, da hadin kai a tsakanin kungiyoyi da al’ummomi daban-daban a yammacin Afirka.

 

NASIR MALALI/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wasa yammacin Afirka

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi

Sojojin kasar Iran sun cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan HKI a dazuda nan nan, wayo yau lahadi a ci gaba da musayar wauta da suke yi da sojojin HKI kwanaki uku da suka gabata.

Kamfanin dillancin  labaran kare kai na kasar Iran Tasnim ya nakalto sojojin kasar na cewa sun cilla makamai masu linzami da Drones a karon farko da rana ido na ganin ido a kan HKI kuma tuna makaman sun fada a inda yakamata su fada a cikin haramtacciyar kasar.

A safiyar ranar jumma’a ce sojojin HKI suka kai hare-hare kan birnin Tehran inda suka kai manya-manyan jami’an sojojin kasar ga shahada, sannan suka kashe mutane fararen hula wadanda basu da laifi.

Bayan haka ne sojojin JMI suka fara maida martani a daren Asabar da daren lahadi, amma a wannan karon sun kai hare haren ne da ranar Lahadi ido na ganin ido.

Hare-haren wadanda aka basu suna “Alkawalin gaskiya Na 3 zasu ci gaba matakar HKI ta ci gaba da kaiwa Iran hare hare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu