Aminiya:
2025-09-18@00:58:38 GMT

Boko Haram ta kashe sojoji 22 da mayaƙan JTF a Borno

Published: 27th, January 2025 GMT

Gomman sojoji da mayaƙan sa-kai na Sibiliyan JTF sun kwanta da dama a wata arangama da mayaƙan Boko Haram a yankin Mai-saleh da ke tsakanin jihohin Borno da Yobe.

Majiyoyin tsaro sun bayyana ce ’yan na Boko Haram sun kai wa jami’an tsaron hari ne bayan da jami’an tsaron sun kwace wani babban sansaninsu da ke Mai-Saleh a tsakanin jihohin biyu.

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro mai barin gado, Manjo-Janar Edward Buba, ya tabbatar da rasuwar sojoji 22 a harin.

“Jimillar sojoji 22 ne suka rasu wasu da dama sun jikkata a yayin artabun,” in ji Edward Buba. Amma wasu majiyoyi sun ce sojojin da suka kwanta dama sun haura 27.

Mace ta rasu, wasu sun jikkata yayin da nakiya ta fashe a Neja ’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Sanarwar da Majo-Janar Edward Buba ya fitar ta ce sojojin sun kashe mayaƙa na musamman na Boko Haram fiye da 70 a yayin artabun.

Ya bayyana cewa kwamandan mayaƙan mai suna Talha da takwarorinsa Abu Yazeed da Malam Umar na daga cikin waɗanda sojoji suka kashe a arangamar ta ranar Asabar.

Edward Buba ya ce sojojin sun kakkaɓo jirage marasa matuƙa na ’yan ta’addan. Ya ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani da ’yan kunar baƙin wake da motoci dauke da abubuwan fashewa ne wajen kai harin.

Ya ce bayan samamen da sojojin suka ƙaddamar domin murƙushe ’yan ta’addan tun ranar 16 ga watan nan na Janairu, sojojin sun kashe ’yan ta’adda sama da 70 sa manyan kwamandojinsu.

 Yadda abin ya faru

Ɗaya da cikin dakarun da suka yi musayar wutar ya shaida wa wakilinmu cewa an kawo musu harin ne bayan da a kusa da wani kududdufi, bayan da suka kwace sansanin Mai-Saleh daga hannun mayaƙan Boko Haram.

“Mun kwace sansanin Mai Saleh wanda ɗaya ne daga cikin manyan sansanonin Boko Haram, amma daga bisani aka kawo mana hari a kusa da ƙoramar.

“A nan ne suka kashe mana kwamanda da sojoji 26 daga Sashe na 2 na Rundunar Operation Hadin Kai. Akwai kuma sojojin da suka jikkata,” in ji shi.

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya ce ya rasa ɗan uwansa da abokan aikinsa biyar a yayin artabun. Ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Ya ce, “gari ya yi duhu lokacin da muka isa ƙoramar, na ji ƙarar wani abu kamar jirgin yaki, sannan ƙarar fashewa.

A kan idona motar da ke gabanmu ta fashe, duk mutanen cikinta suka mutu, yana mai cewa yawan mamatan na iya ƙaruwa.

Shi ma wani soja da ta ce adadin mamatan na iya ƙaruwa, ya bayyana cewa abokan aikinsa da dama sun rasu a harin, domin “babu wanda zai iya faɗan haƙiƙanin yawan waɗanda suka rasu saboda akwai mafarauta da Sibiliyan JTF da sojoji daga Goniri, Buni Yadi, Damboa da Sabon Gari da aka yi aikin tare da su.

Daga Hamisu Kabir Matazu (Maiduguri); Sagir Kano Saleh & Idowu Isamotu (Abuja)

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin

Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.

Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.

Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II

“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.

Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.

Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.

Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.

Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren  ibada da gidajen marayu.

Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.

Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa