Aminiya:
2025-04-30@19:56:17 GMT

Boko Haram ta kashe sojoji 22 da mayaƙan JTF a Borno

Published: 27th, January 2025 GMT

Gomman sojoji da mayaƙan sa-kai na Sibiliyan JTF sun kwanta da dama a wata arangama da mayaƙan Boko Haram a yankin Mai-saleh da ke tsakanin jihohin Borno da Yobe.

Majiyoyin tsaro sun bayyana ce ’yan na Boko Haram sun kai wa jami’an tsaron hari ne bayan da jami’an tsaron sun kwace wani babban sansaninsu da ke Mai-Saleh a tsakanin jihohin biyu.

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro mai barin gado, Manjo-Janar Edward Buba, ya tabbatar da rasuwar sojoji 22 a harin.

“Jimillar sojoji 22 ne suka rasu wasu da dama sun jikkata a yayin artabun,” in ji Edward Buba. Amma wasu majiyoyi sun ce sojojin da suka kwanta dama sun haura 27.

Mace ta rasu, wasu sun jikkata yayin da nakiya ta fashe a Neja ’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Sanarwar da Majo-Janar Edward Buba ya fitar ta ce sojojin sun kashe mayaƙa na musamman na Boko Haram fiye da 70 a yayin artabun.

Ya bayyana cewa kwamandan mayaƙan mai suna Talha da takwarorinsa Abu Yazeed da Malam Umar na daga cikin waɗanda sojoji suka kashe a arangamar ta ranar Asabar.

Edward Buba ya ce sojojin sun kakkaɓo jirage marasa matuƙa na ’yan ta’addan. Ya ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani da ’yan kunar baƙin wake da motoci dauke da abubuwan fashewa ne wajen kai harin.

Ya ce bayan samamen da sojojin suka ƙaddamar domin murƙushe ’yan ta’addan tun ranar 16 ga watan nan na Janairu, sojojin sun kashe ’yan ta’adda sama da 70 sa manyan kwamandojinsu.

 Yadda abin ya faru

Ɗaya da cikin dakarun da suka yi musayar wutar ya shaida wa wakilinmu cewa an kawo musu harin ne bayan da a kusa da wani kududdufi, bayan da suka kwace sansanin Mai-Saleh daga hannun mayaƙan Boko Haram.

“Mun kwace sansanin Mai Saleh wanda ɗaya ne daga cikin manyan sansanonin Boko Haram, amma daga bisani aka kawo mana hari a kusa da ƙoramar.

“A nan ne suka kashe mana kwamanda da sojoji 26 daga Sashe na 2 na Rundunar Operation Hadin Kai. Akwai kuma sojojin da suka jikkata,” in ji shi.

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya ce ya rasa ɗan uwansa da abokan aikinsa biyar a yayin artabun. Ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Ya ce, “gari ya yi duhu lokacin da muka isa ƙoramar, na ji ƙarar wani abu kamar jirgin yaki, sannan ƙarar fashewa.

A kan idona motar da ke gabanmu ta fashe, duk mutanen cikinta suka mutu, yana mai cewa yawan mamatan na iya ƙaruwa.

Shi ma wani soja da ta ce adadin mamatan na iya ƙaruwa, ya bayyana cewa abokan aikinsa da dama sun rasu a harin, domin “babu wanda zai iya faɗan haƙiƙanin yawan waɗanda suka rasu saboda akwai mafarauta da Sibiliyan JTF da sojoji daga Goniri, Buni Yadi, Damboa da Sabon Gari da aka yi aikin tare da su.

Daga Hamisu Kabir Matazu (Maiduguri); Sagir Kano Saleh & Idowu Isamotu (Abuja)

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

 Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6

Wani bon kirar hannu da aka dasa akan hanyar dake hada Rann da Gamboru a jihar Borno ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 6.

Daga cikin wadanda su ka rasa rayukansu sanadiyyar tashin bom din sun hada mata da kananan yara kamar yadda majiyar ‘yan sanda ta sanar.

Kungiyar nan mai suna; gwamnatin musulunci a yammacin Afirka ce ta sanar da daukar alhakin kai hari na ranar Litinin din da ta gabata.

Bugu da kari sauran wadanda su ka rasa rayukan nasu manoma ne da suke cikin motar a-kori-kura da ta taka nakiya.

Baya ga wadanda su ka rasa rayukansu, wasu mutanen su 3 sun jikkata,kuma tuni an dauke su zuwa asibiti domin yi musu magani.

Wani dan sintiri da yake aiki da rundunar fararen hula masu taimakawa jami’an tsaro, Abba Madu, ya shaida wa manema labaru cewa; Da alamu an dasa bom din domin ya tashi da jami’an tsaro da suke yin sintiri akan wannan hanyar.

Kungiyoyin ‘yan ta’adda sun saba dasa irin wadannan nakiyoyin da bama-baman akan hanyar da jami’an tsaro suke bi.

Kungiyar nan da take kiran kanta; Gwamnatin Musulunci a yammacin Afirka wacce a takaice ake kira; “ISWAP” ce ta dauki nauyin kai harin.

Tun a 2009 ne yankin Arewa maso gabashin kasar ta Najeriya yake fama da matsalar kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada Bokoharam, sannan kuma daga baya waje 2016, kungiyar gwamnatin musulunci a yammacin Afirka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno