Aminiya:
2025-11-03@08:13:37 GMT

Boko Haram ta kashe sojoji 22 da mayaƙan JTF a Borno

Published: 27th, January 2025 GMT

Gomman sojoji da mayaƙan sa-kai na Sibiliyan JTF sun kwanta da dama a wata arangama da mayaƙan Boko Haram a yankin Mai-saleh da ke tsakanin jihohin Borno da Yobe.

Majiyoyin tsaro sun bayyana ce ’yan na Boko Haram sun kai wa jami’an tsaron hari ne bayan da jami’an tsaron sun kwace wani babban sansaninsu da ke Mai-Saleh a tsakanin jihohin biyu.

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro mai barin gado, Manjo-Janar Edward Buba, ya tabbatar da rasuwar sojoji 22 a harin.

“Jimillar sojoji 22 ne suka rasu wasu da dama sun jikkata a yayin artabun,” in ji Edward Buba. Amma wasu majiyoyi sun ce sojojin da suka kwanta dama sun haura 27.

Mace ta rasu, wasu sun jikkata yayin da nakiya ta fashe a Neja ’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Sanarwar da Majo-Janar Edward Buba ya fitar ta ce sojojin sun kashe mayaƙa na musamman na Boko Haram fiye da 70 a yayin artabun.

Ya bayyana cewa kwamandan mayaƙan mai suna Talha da takwarorinsa Abu Yazeed da Malam Umar na daga cikin waɗanda sojoji suka kashe a arangamar ta ranar Asabar.

Edward Buba ya ce sojojin sun kakkaɓo jirage marasa matuƙa na ’yan ta’addan. Ya ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani da ’yan kunar baƙin wake da motoci dauke da abubuwan fashewa ne wajen kai harin.

Ya ce bayan samamen da sojojin suka ƙaddamar domin murƙushe ’yan ta’addan tun ranar 16 ga watan nan na Janairu, sojojin sun kashe ’yan ta’adda sama da 70 sa manyan kwamandojinsu.

 Yadda abin ya faru

Ɗaya da cikin dakarun da suka yi musayar wutar ya shaida wa wakilinmu cewa an kawo musu harin ne bayan da a kusa da wani kududdufi, bayan da suka kwace sansanin Mai-Saleh daga hannun mayaƙan Boko Haram.

“Mun kwace sansanin Mai Saleh wanda ɗaya ne daga cikin manyan sansanonin Boko Haram, amma daga bisani aka kawo mana hari a kusa da ƙoramar.

“A nan ne suka kashe mana kwamanda da sojoji 26 daga Sashe na 2 na Rundunar Operation Hadin Kai. Akwai kuma sojojin da suka jikkata,” in ji shi.

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya ce ya rasa ɗan uwansa da abokan aikinsa biyar a yayin artabun. Ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Ya ce, “gari ya yi duhu lokacin da muka isa ƙoramar, na ji ƙarar wani abu kamar jirgin yaki, sannan ƙarar fashewa.

A kan idona motar da ke gabanmu ta fashe, duk mutanen cikinta suka mutu, yana mai cewa yawan mamatan na iya ƙaruwa.

Shi ma wani soja da ta ce adadin mamatan na iya ƙaruwa, ya bayyana cewa abokan aikinsa da dama sun rasu a harin, domin “babu wanda zai iya faɗan haƙiƙanin yawan waɗanda suka rasu saboda akwai mafarauta da Sibiliyan JTF da sojoji daga Goniri, Buni Yadi, Damboa da Sabon Gari da aka yi aikin tare da su.

Daga Hamisu Kabir Matazu (Maiduguri); Sagir Kano Saleh & Idowu Isamotu (Abuja)

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka

Wani sojan Ƙasar Amurka ɗan asalin Jihar Kano, Suleiman Isah, wanda yake aiki a rundunar sojin Amurka, ya ce ba zai yaƙi da ƙasarsa ta haihuwa ba saboda yaɗa labaran ƙarya game da yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.

Isah, wanda ya shiga rundunar sojin Amurka shekaru biyu da suka gabata, yana aiki ne da rundunar California Army National Guard, mai dakaru sama da 18,000.

Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook wanda Aminiya ta tabbatar, Isah ya mayar da martani kan jita-jitar cewa Amurka za ta ɗauki matakin yaƙi a kan Najeriya saboda zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.

Ya bayyana cewa ba zai taɓa amfani da makami a kan mutanensa ba.

“Ba zan shiga Najeriya na kashe iyayena ba saboda ƙaryar cewa ana kashe Kiristoci,” in ji shi.

Ya ce duk da yake yana Allah-wadai da kashe-kashe da tashin hankali, bai kamata matsalar tsaro a Najeriya a danganta da wani addini ba.

“Ba zan ƙaryata batun kisan Kiristoci da Musulmai ba,” in ji shi.

“Shekau, Bello Turji, Dogo Gide da sauransu ba suna kai wa wani addini ɗaya hari ba ne kaɗai.”

Maganganun Isah na zuwa ne daidai lokacin Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi a kan Najeriya.

Sai dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini ba ce, inda ta ce matsalar na shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m