Aminiya:
2025-06-15@02:17:57 GMT

Boko Haram ta kashe sojoji 22 da mayaƙan JTF a Borno

Published: 27th, January 2025 GMT

Gomman sojoji da mayaƙan sa-kai na Sibiliyan JTF sun kwanta da dama a wata arangama da mayaƙan Boko Haram a yankin Mai-saleh da ke tsakanin jihohin Borno da Yobe.

Majiyoyin tsaro sun bayyana ce ’yan na Boko Haram sun kai wa jami’an tsaron hari ne bayan da jami’an tsaron sun kwace wani babban sansaninsu da ke Mai-Saleh a tsakanin jihohin biyu.

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro mai barin gado, Manjo-Janar Edward Buba, ya tabbatar da rasuwar sojoji 22 a harin.

“Jimillar sojoji 22 ne suka rasu wasu da dama sun jikkata a yayin artabun,” in ji Edward Buba. Amma wasu majiyoyi sun ce sojojin da suka kwanta dama sun haura 27.

Mace ta rasu, wasu sun jikkata yayin da nakiya ta fashe a Neja ’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Sanarwar da Majo-Janar Edward Buba ya fitar ta ce sojojin sun kashe mayaƙa na musamman na Boko Haram fiye da 70 a yayin artabun.

Ya bayyana cewa kwamandan mayaƙan mai suna Talha da takwarorinsa Abu Yazeed da Malam Umar na daga cikin waɗanda sojoji suka kashe a arangamar ta ranar Asabar.

Edward Buba ya ce sojojin sun kakkaɓo jirage marasa matuƙa na ’yan ta’addan. Ya ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani da ’yan kunar baƙin wake da motoci dauke da abubuwan fashewa ne wajen kai harin.

Ya ce bayan samamen da sojojin suka ƙaddamar domin murƙushe ’yan ta’addan tun ranar 16 ga watan nan na Janairu, sojojin sun kashe ’yan ta’adda sama da 70 sa manyan kwamandojinsu.

 Yadda abin ya faru

Ɗaya da cikin dakarun da suka yi musayar wutar ya shaida wa wakilinmu cewa an kawo musu harin ne bayan da a kusa da wani kududdufi, bayan da suka kwace sansanin Mai-Saleh daga hannun mayaƙan Boko Haram.

“Mun kwace sansanin Mai Saleh wanda ɗaya ne daga cikin manyan sansanonin Boko Haram, amma daga bisani aka kawo mana hari a kusa da ƙoramar.

“A nan ne suka kashe mana kwamanda da sojoji 26 daga Sashe na 2 na Rundunar Operation Hadin Kai. Akwai kuma sojojin da suka jikkata,” in ji shi.

Wani jami’in Sibiliyan JTF ya ce ya rasa ɗan uwansa da abokan aikinsa biyar a yayin artabun. Ya bayyana cewa maharan sun kawo musu harin ne makaman RPG da ’yan ƙunar baƙin wake da jirage marasa matuƙa wajen halaka jami’an tsaron.

Ya ce, “gari ya yi duhu lokacin da muka isa ƙoramar, na ji ƙarar wani abu kamar jirgin yaki, sannan ƙarar fashewa.

A kan idona motar da ke gabanmu ta fashe, duk mutanen cikinta suka mutu, yana mai cewa yawan mamatan na iya ƙaruwa.

Shi ma wani soja da ta ce adadin mamatan na iya ƙaruwa, ya bayyana cewa abokan aikinsa da dama sun rasu a harin, domin “babu wanda zai iya faɗan haƙiƙanin yawan waɗanda suka rasu saboda akwai mafarauta da Sibiliyan JTF da sojoji daga Goniri, Buni Yadi, Damboa da Sabon Gari da aka yi aikin tare da su.

Daga Hamisu Kabir Matazu (Maiduguri); Sagir Kano Saleh & Idowu Isamotu (Abuja)

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.

Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.

“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.

“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”

Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.

Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.

Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.

“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.

“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”

Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.

Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.

Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.

“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.

“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”

Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita