Aminiya:
2025-09-17@23:15:03 GMT

Ƙungiyoyin da za su fafata da juna a Copa del Rey

Published: 26th, January 2025 GMT

Real Madrid za ta fafata da Leganes, yayin da Barcelona za ta je Valencia a zagayen kwata fainal a Copa del Rey, bayan da aka raba jadawali ranar Litinin.

Wani wasan da zai yi zafi shi ne tsakanin Atletico Madrid da Getafe, yayin da za a yi tata-ɓurza tsakanin Real Sociedad da Osasuna.

Shin wannan ce kaka mafi muni ga Man-United a Gasar Firimiya? Gobarar tankar mai ta yi ajalin mutum 18 a Enugu

Ana sa ran buga wasannin da za a gudanar ranar 5 ga watan Fabrairu.

A jadawalin ya bayar da damar sake buga El Clasico wato karawar hamayya tsakanin Real da Barcelona a wasan ƙarshe da suka daɗe ba su haɗu a gasar tsawon shekaru.

An haɗu a wasan karshe a Copa del Rey karawar El Clasico sau 18, Real ce ta yi nasara 11 daga ciki, wasan baya bayan nan da suka kara shi ne a 2014. Kuma Real Madrid ce ta lashe kofin da cin 2-1 a wasan da aka yi a Valencia.

Sai dai a kakar bana, Barcelona ta caskara Real Madrid karo biyu a baya, wadda ta fara cin 4-0 a Santiago Bernabeu cikin watan Oktoban 2024.

Sai kuma Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na bana a kan Real Madrid da cin 5-2 a Saudi Arabia a makon jiya.

Real Madrid ce kan gaba a teburin La Liga da maki 46, sai Atletico Madrid ta biyu da kuma Barcelona ta uku da tazarar maki makwai tsakani da Real.

Barcelona za ta je gidan Valencia a Copa del Rey zagayen kwata fainal, kamar yadda aka raba jaddawali ranar Litinin.

Barcelona ta kawo wannan matakin, sakamakon nasara a kan Real Betis 5-1 ranar Laraba 15 ga watan Janairu a zagayen ‘yan 16.

Ita kuwa Valencia zuwa ta yi ta doke Ourense 2-0 ranar Talata 14 ga watan Janairu.

Valencia da Barcelona za su fuskanci juna a zagayen ’yan takwas ranar Laraba 5 ga watan Fabrairu a filin wasa da ake kira Mestalla.

Jadawalin kwata fainal a Copa del Rey:

Leganes da Real Madrid

Atlético Madrid da Getafe

Real Sociedad da Osasuna

Valencia da Barcelona

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya gudanar da taron manema labarai da misalin karfe 10 na safiyar yau Litinin, inda kakakin hukumar kididdiga ta kasar, kuma babban masanin tattalin arziki, kana daraktan sashen kididdigar tattalin arziki na kasar, Fu Linghui ya yi karin haske kan ayyukan tattalin arzikin kasar cikin watan Agustan bana, tare da amsa tambayoyin manema labarai.

A cewar bayanan da aka gabatar a yayin taron, ayyukan tattalin arzikin kasar a watan Agusta sun samu ci gaba ba tare da tangarda ba. Kuma hakan ya bayyana ne ta hanyoyi daban-daban kamar haka: masana’antu sun habaka cikin sauri, masana’antar kera kayayyakin aiki da masana’antar fasaha sun samu ci gaba mai kyau. Kana ayyukan bayar da hidima su ma sun bunkasa cikin sauri. Baya ga haka, an samu ci gaba mai kyau a bangaren bayar da hidimomi na zamani. Harkokin kasuwanci sun samu ci gaba cikin natsuwa, inda harkokin sayar da kayayyaki ga masu sayayya suka kara habaka. Har ila yau, kadarorin jari sun ci gaba da karuwa, jarin masana’antu ya habaka cikin sauri, harkokin fice da shigen kayayyaki sun ci gaba da girma, tsarin kasuwanci ya ci gaba da ingantuwa, kana yanayin samar da guraben aikin yi, ya kasance kan wani mataki mai daidaito. Sai dai kuma saboda yanayin da ake ciki, adadin marasa aikin yi a birane ya karu, ma’aunin Core CPI ya ci gaba da hauhawa, kana faduwar farashin kayayyakin masana’antu ya ragu.

Bayanan sun kara da cewa, akwai bukatar lura da cewa, ana fuskantar yanayin rashin tabbas a waje, kuma tattalin arzikin kasar Sin yana fuskantar kalubale da hadari da yawa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff