Aminiya:
2025-09-17@21:51:30 GMT

Injin niƙa ya yi ajalin matar aure mai ’ya’ya 6 a Gombe

Published: 10th, September 2025 GMT

Injin nika shinkafa ya yi ajalin wata mata mai shekaru 32, Hauwau Abubakar a kauyen Tumu da ke karamar hukumar Akkon jihar Gombe.

Lamarin ya faru a lokacin da marigayiyar mai ’ya’ya shida ta je sayen shinkafa wajen wani mai injin mai suna Muhammad Danjuma mai shekaru 29.

Bayanan Rundunar ’Yan Sandan Jihar sun nuna cewa hijabin jikinta ne ya kama bel ɗin injin, sannan ya ja ta jikinsa ya ji mata rauni a wuya, lamarin da ya yi sanadin mutuwarta nan take.

Mamakon ruwan sama ya hallaka mutum 3 a Zariya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

Daga nan ne aka garzaya da ita zuwa asibitin garin na Tumu, inda likita ya tabbatar da mutuwarta, daga nan kuma aka mika gawarta ga iyalinta domin yi mata jana’iza bisa tsarin addinin Musulunci.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Bello Yahaya, ya bayyana alhininsa tare da jajanta wa iyalan marigayiyar da al’ummar garin baki ɗaya, yana mai cewa lamarin babban rashi ne kuma mai tayar da hankali.

A wani bangare kuma, rundunar ta shawarci masu injinan nika, ma’aikata da ’yan kasuwa da su kula da ka’idojin tsaro yayin da suke aiki da irin waɗannan injinan.

Shawarwarin sun haɗa da tabbatar da kulawa yayin da injina ke aiki, da kuma hana yara kusantar irin waɗannan na’urori.

Rundunar ta kuma bukaci jama’a da su rika bayar da rahoton rashin bin matakan tsaro wajen amfani da injina, domin kaucewa afkuwar irin wannan mummunan hatsari a nan gaba.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya tabbatar da cewa: “Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da tabbatar da tsaron jama’a a kowane lokaci.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.

Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.

Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.

“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.

Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.

Gwamnan ya kuma sake jaddada  cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.

Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha