An kai wa tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami hari a Kebbi
Published: 2nd, September 2025 GMT
Tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami ya tsallake rijiya da baya a garin Birnin Kebbi yayin da wasu matasa suka kai wa tawagarsa hari.
Abubakar Malami da tawagarsa, wasu ’yan bangar siyasa sun tare su, a unguwar GRA, inda suka yi amfani da sanduna da addun da sanduna suka farfasa motocin Malami tare da jikkata mutanensa, Kodayake babu asarar rai.
Bayan dawowar tsohon ministan a zamanin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, gida ya yi zargin siyasa ce ta a da aka kai masa harin, yana mai jaddada cewa, harkar siyasarsa babu gudu babu ja da baya.
“Shari’a ta tanadi ka kare kai, in aka kawo maka hari amma kai kar ka kai wa kowa hari, maganar siyasa ba gudu ba ja da baya.
Girgizar ƙasa ta hallaka fiye da mutum 800 a Afghanistan An kama uba da ɗansa kan yi wa ’yar shekara 13 fyaɗe a Gombe“Muna da hakkin kare kai in an ture mu, kariyar kai a shari’ar Musulunci hakki ne, mai girma Gwamna ya ce ya bude littafin siyasa mu ko mun fara karatu,” a cewar Malami, a jawabinsa ga magoya bayansa.
Ya zargi magoya bayan Jam’iyyar APC da kai masu hari, “addini ya aminta mu yi wa ’yan uwa jaje in sun samu rashi, shi ne maƙasudin yin wannan ziyara a garin Birnin Kebbi, bakin abubuwa marasa dadi sun bayyana wadanda suke da nasaba da siyasa, bayyane take mutane sun fito daga hedikwatar Jam’iyyar APC ɗauke da miyagun makamai suna jifan abokan hamayya.”
Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kebbi Yakubu Ahmed ya ce ba zai ce komai ba kan zargin, magana ce ta jam’iyya don haka a tuntube jami’yya.
Wakilinmu ya tuntubi Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Kana a waya amma bai daga ba, ya kuma tura masa sako bai ce komai ba, ya sake kiran sa, amma ya ji ‘number busy.’
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kebbi, Bello Sani, ya ce ba wani da aka kama kan harin da aka kai wa tawagar tsohon minista Malami.
A lokacin da yake magana da manema labarai bayan ya kammala zama da Gwamna kan matslar tsaro, Kwamishinan ’yan sandan ya ce ana gudanar da bincike kan abin da ya faru.
A cewarsa, gwamnan ya kira taro kan tsaro game da abin da ya faru a unguwar G.R.A inda wasu ’yan jami’yyu suka karya doka da yin wasu al’amurran yakin neman zaɓe.
Ya ce “dole ne mu gayyaci jam’iyun siyasa mu tattauna don su san har yanzu ba a dage shingen fara yekuwar zabe ba.”
Kwamishina ya ce ’yan sanda sun sanya dakaru da za su hana duk wani yekuwar zaɓe don haka yana kira ga jam’iyyun siyasa su kwantar da hankalinsu.
“Abin da ya faru ana kan bincike kuma duk wanda aka samu da laifi za a kama shi ya fuskanci Shari’a,” in ji Kwamishina.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Duk da cewa suna da karfi a fannin aikin soja, amma harinsu zai zama tamkar amfani da igwa ne wajen kashe sauro. Duk wani fifikon da suke da shi ba zai dore ba. Saboda haka, a zahiri wannan tambayar da wani mai amfani da yanar gizo ya yi, ta nuna rashin hankali cikin kalaman shugaban Amurka.
Sai dai kalaman sun dace da halayya, da salon musamman na shugaba Donald Trump. Wani lokaci, da gangan ya kan yi amfani da kalmomi, da aikace-aikace marasa ma’ana wajen samar da yanayi na rashin tabbas, ta yadda zai samu damar matsawa wani lamba, don tilasta masa ya yi wani aiki. Wannan dabara ce da wasu masanan kasar Amurka ke kira da “ka’idar mahaukaci”, watakila ta dace da halayyar shugaba Trump, abun da ya sa yake ta amfani da ita wajen kula da harkokin waje.
Kana wannan batu na yin barazanar kai hari ya dace da halayyar kasar Amurka. Kasa ce wadda ba ta mai da hankali a kan neman gano gaskiya ba, balle ma la’akari da bayanan da Nijeriya ta gabatar dangane da zargin da aka yi mata. Kai tsaye an yi fatali da ikon mulkin kai na Najeriya, da dokokin kasa da kasa, da ra’ayoyin kasashen yankin da ake ciki. A ganin kasar Amurka, tana iya tsoma baki a duk wani aiki, da aikata yadda ta ga dama, kuma idan za ta iya yin amfani da karfin tuwo wajen tilasta wani, to ba za ta taba tattaunawa da shi ba. Kawai kasar tana kokarin aiwatar da mulkin danniya ne a duniya.
Amma, a cewar wasu masana, “ka’idar mahaukaci” ba ko yaushe take yin tasiri ba. Saboda idan wani ya dade yana kwaikwayon mahaukaci, to, ba za a ci gaba da tsoronsa ba. Kana mulkin danniya na kasar Amurka shi ma ba zai dore ba, idan aka yi la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke tasowa cikin sauri a zamanin da muke ciki.
Ko ta yaya ya kamata Amurka ta daidaita kalamanta da ayyukanta? Kuma ta wace hanya ya kamata kasashe daban daban su yi mu’ammala da juna?
Na farko, ya kamata mu tabbatar da daidaito tsakanin mabambanta kasashe, da kuma bin dokokin kasa da kasa. Na biyu, ya kamata mu daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da neman daidaita harkoki ta hanyar yin shawarwari, maimakon tayar da rikici. Na uku, ya kamata mu dora muhimmanci kan jin dadin jama’a, ta yadda ba za a tsaya ga kula da mutanen gida kadai ba, wato a hada da al’ummun sauran kasashe. Ya kamata a lura da hakkinsu da bukatunsu. Wadannan abubuwa suna cikin shawarar da kasar Sin ta gabatar, dangane da inganta jagorancin duniya.
Watakila kasar Amurka ba ta yarda da wadannan ka’idoji ba tukuna, amma tabbas wata rana za ta amince da su. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA