Aminiya:
2025-09-17@21:49:48 GMT

Tsohon Sufeto-Janar na ’yanyan sandan Nijeriya Solomon Arase ya rasu

Published: 31st, August 2025 GMT

Tsohon Sufeto-Janar na rundunar ’yan sandan Nijeriya, Solomon Arase ya riga mu gidan gaskiya a Abuja, babban birnin kasar.

Rahotanni sun ce tsohon IG din ya rasu ne a Asibitin Cedarcrest da ke Abuja a safiyar Lahadin nan.

An ƙone wata mata ƙurmus kan yi wa Annabi ɓatanci a Neja Chelsea ta kammala ɗaukar Garnacho daga Manchester United

Kawo yanzu dai iyalai ko rundunar ’yan sandan kasar ba su fitar da rahoton rasuwar a hukumance ba, sai dai wani hadiminsa da Aminiya ta tuntuba ya tabbatar da hakan.

Arase wanda tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya nada a Afrilun 2015 shi ne Sufeto Janar na 18 a tarihin Nijeriya.

Kazalika, bayan ritayarsa a shekarar 2016, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada shi shugaban hukumar kula da harkokin ’yan sanda ta Nijeriya PSC a Janairun 2023, wanda kuma shugaba Bola Tinubu ya sauke a bara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Solomon Arase

এছাড়াও পড়ুন:

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sun jaddada cewa dole ne manyan kafafen sada zumunta su kare ‘yancin yin magana.

Sun kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, ‘yan jarida, da masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama su tashi tsaye don hana abin da suka kira yunƙurin mayar da Nijeriya “mulkin kama-karya a intanet.”

Lamarin ya biyo bayan wa’adin sati guda da DSS ta bai wa Sowore da ya goge wasu wasu rubuce-rubuce game da Shugaba Bola Tinubu, wanda ya ƙi amincewa.

Hakan ya sa hukumar ta shigar da shi ƙara a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja