An kashe makiyaya 4, an jikkata wani a Filato
Published: 29th, August 2025 GMT
An kashe makiyaya huɗu tare da jikkata wani a ƙauyen Fili, da ke yankin Doemak, a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan a Jihar Filato.
Rahotanni daga yankin sun ce an kai musu hari ne lokacin da suke tsaka da kiwo.
Na bar APC saboda Tinubu bai cika alƙawarin da ya yi ba — Marafa An kama wani mutum da laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maitaSakataren kuɗi na Ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) a Qua’an Pan, Saeedu Abdurrahman, ya tabbatar da lamarin.
Ya ce ’yan bindigar sun kashe makiyayan amma ba su sace shanunsu ba.
Ya ƙara da cewa lokacin da ake binne waɗanda suka rasu, ’yan bindigar sun sake kai wani harin, amma jami’an tsaro sun daƙile harin.
Ɗan uwan ɗaya daga cikin waɗanda harin ya rutsa da su, Shanono Muhammad, ya ce, “An kashe makiyaya huɗu, ciki har da ƙaramin yaro da ya tafi koyon kiwon shanu.
’An kashe su ne da yammacin ranar Talata yayin da suke kiwo.”
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, mai magana da yawun Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai yi ƙarin haske kan harin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari mahara Makiyaya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025
Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025
Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025