Aminiya:
2025-09-17@20:28:31 GMT

An kama wani mutum da laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maita

Published: 29th, August 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama wani matashi ɗan shekara 25 mai suna Jibrin Ado bisa laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maita a unguwar Gerawa da ke jihar.

Majiyar PUNCH ta ruwaito hakan ne a ranar Alhamis daga wata sanarwa ta manhajar X ta wani masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama.

Ambaliya ta raba ƙauyukan Sakkwato 6 da sauran sassan jihar An fara gyaran layin dogon Abuja-Kaduna bayan hatsarin jirgin ƙasa

A cewarsa, Ado ya aikata wannan aika-aika ne tare da wasu masu laifin a ranar Talata.

Waɗanda suka haɗa da: Musa Kwalle da Dan Abba da Sule Musa da wani Arrow dukkansu daga ƙauyen Gerawa.

Majiyar ta bayyana cewa, a ranar 26 ga watan Agusta da misalin ƙarfe 4:30 na yamma, wanda ake zargin mai suna Jibrin Ado na ƙauyen Daneji, ya haɗa baki da wasu – Musa Kwalle da Ɗan Abba, Sule Musa da Arrow, dukkansu ’yan ƙauyen Gerawa, inda suka shiga gidan mahaifinsa, Adamu Saleh.

“Waɗanda ake zargin sun yi wa matarsa (Saleh) duka, Magajiya Ado, ‘yar shekara 50 da manyan sanduna har sai da ta sume, suna zarginta da maita,” ya rubuta.

Makama ya ci gaba da cewa, an garzaya da mamaciyar zuwa babban asibitin unguwar Ringim da ke unguwar, inda ta rasu a lokacin da take jinya.

“Majiyoyi sun ce tuni aka sako gawarta ga ’yan uwa don binne ta, majiyar ta ƙara da cewa an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin Jibrin Ado, yayin da sauran kuma ke hannunsu”.

Da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Lawan Shiisu ya yi alƙawarin binciken lamarin tare da yin ƙarin bayani nan gaba. Har yanzu bai yi haka ba har zuwa lokacin da aka gabatar da rahoton.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gerawa Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar