Aminiya:
2025-11-03@00:49:11 GMT

Sanusi Mikail Sami ya zama sabon Sarkin Zuru

Published: 28th, August 2025 GMT

Alhaji Sanusi Mikail Sami Gomo na III ya zama sabon Sarkin Zuru.

Kwamishinan Ƙananan hukumomi da masarautu, Alhaji Abubakar Garba Dutsin-Mari ne ya sanar da hakan yau Alhamis, a fadar Sarkin Zuru wanda kuma ya miƙa masa takardar naɗin da Gwamnan Kebbi, Nasir Idris ya sanya wa hannu.

Ambaliya: Manoma sun yi asarar miliyoyin Naira a Taraba ACF ta yi Allah-wadai da rushe kasuwar Alaba Rago

Ya ce, naɗin sabon Sarkin ya biyo bayan miƙa sunayen sarakuna uku da  masarautar Zuru ta miƙa wa Gwamnan jihar, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Ya ƙara da cewa, Gwamnan wajen yin amfani da ikon da aka ba shi, ya amince da Alhaji Sanusi Mikail Sami a matsayin sabon Sarkin Zuru, wanda yanzu aka amince da shi a matsayin Gomo III.

Tun da farko, Sarkin Wasagu, Alhaji Muktari Musa wanda ya riƙe muƙamin muƙaddashin Sarki tun bayan rasuwar marigayin, ya karɓi baƙoncin sabon Sarkin a hukumance tare da maraba da dukkan baƙi a fadar.

A nasa jawabin, sabon Sarkin ya nuna godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki da kuma Gwamna Nasir Idris bisa amincewar da aka yi masa.

Ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu zaman lafiya da aminci da kuma haɗin kai, yana mai ba su tabbacin buɗaɗɗiyar manufarsu da kuma jagoranci na bai ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sarkin Zuru sabon Sarkin Sarkin Zuru

এছাড়াও পড়ুন:

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

 

Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu November 2, 2025 Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi