Sanusi Mikail Sami ya zama sabon Sarkin Zuru
Published: 28th, August 2025 GMT
Alhaji Sanusi Mikail Sami Gomo na III ya zama sabon Sarkin Zuru.
Kwamishinan Ƙananan hukumomi da masarautu, Alhaji Abubakar Garba Dutsin-Mari ne ya sanar da hakan yau Alhamis, a fadar Sarkin Zuru wanda kuma ya miƙa masa takardar naɗin da Gwamnan Kebbi, Nasir Idris ya sanya wa hannu.
Ambaliya: Manoma sun yi asarar miliyoyin Naira a Taraba ACF ta yi Allah-wadai da rushe kasuwar Alaba RagoYa ce, naɗin sabon Sarkin ya biyo bayan miƙa sunayen sarakuna uku da masarautar Zuru ta miƙa wa Gwamnan jihar, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
Ya ƙara da cewa, Gwamnan wajen yin amfani da ikon da aka ba shi, ya amince da Alhaji Sanusi Mikail Sami a matsayin sabon Sarkin Zuru, wanda yanzu aka amince da shi a matsayin Gomo III.
Tun da farko, Sarkin Wasagu, Alhaji Muktari Musa wanda ya riƙe muƙamin muƙaddashin Sarki tun bayan rasuwar marigayin, ya karɓi baƙoncin sabon Sarkin a hukumance tare da maraba da dukkan baƙi a fadar.
A nasa jawabin, sabon Sarkin ya nuna godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki da kuma Gwamna Nasir Idris bisa amincewar da aka yi masa.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu zaman lafiya da aminci da kuma haɗin kai, yana mai ba su tabbacin buɗaɗɗiyar manufarsu da kuma jagoranci na bai ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sarkin Zuru sabon Sarkin Sarkin Zuru
এছাড়াও পড়ুন:
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA