Aminiya:
2025-05-19@18:09:03 GMT

Mataimakiyar shugaban majalisar dokokin Edo ta yi murabus

Published: 19th, May 2025 GMT

Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Edo, Misis Maria Oligbi-Edeko, ta ajiye muƙaminta.

Ta bayyana murabus ɗinta ne a zaman majalisar da aka yi a ranar Litinin a Birnin Benin, babban birnin jihar.

Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200

Oligbi-Edeko, wadda ke wakiltar mazaɓar Esan ta Arewa Maso Gabas II, ta ce ta yi murabus ne, saboda jam’iyyarta ta PDP ta rasa rinjaye a majalisar bayan wasu ’yan jam’iyyar ciki har da Shugaban Majalisar sun koma jam’iyyar APC.

An zaɓe ta a matsayin Mataimakiyar Shugaban Majalisar karo na takwas a ranar 16 ga watan Yunin 2023, kafin ta yi murabus.

Bayan ta yi murabus, majalisar ta zaɓi Mista Osamwonyi Atu daga jam’iyyar APC (Orhionmwon ta Gabas) a matsayin sabon mataimakin shugaban majalisar.

Jagoran Majalisar, Hon. Jonathan Aigbokhan, ya gabatar da ƙuduri cewa a ci gaba da biyanta dukkanin haƙƙoƙinta da ke tattare da kujerar mataimakiyar shugaban majalisar.

Wannan ƙuduri ya samu goyon bayan shugaban ’yan adawa, Hon. Charity Airobarueghian, kuma dukkanin ‘yan majalisar sun amince da shi.

A cikin wasiƙar murabus ɗinta, Oligbi-Edeko ta ce ta yi hakan ne domin tabbatar da adalci, gaskiya da daidaito ga dukkanin mazaɓu.

Ta kuma gode wa shugabanni da mambobin jam’iyyar PDP saboda damar da suka bata ta wakilci mazaɓarta.

’Yan majalisar sun yaba da ƙoƙarinta da jajircewarta wajen yi wa jama’a hidima.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Mataimakiyar Shugaban Majalisa Murabus Siyasa shugaban majalisar ta yi murabus

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta yi barazanar kashe shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen

Gwamnatin Isra’ila ta yi barazanar kashe jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Abdul-Malik al-Houthi, idan har Sana’a ta ci gaba da kai hare-hare da makami mai linzami kan Isra’ilar don goyon bayan Falasdinu.

Ministan harkokin soji na gwamnatin, Isra’ila Katz ya ce idan har Yemen ta ci gaba da ayyukanta “za su sha azaba mai radadi.” 

Katz ya ce kisan da gwamnatin za ta wa al-Houthi zai yi kama da kisan gilla kan “Deif da Sinwars a Gaza.”

Ministan na Isra’ila yana magana ne a kan tsohon kwamandan kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da ke Zirin Gaza, Mohammed Deif, wanda gwamnatin kasar ta sanar da kashe shi a watan Janairu.

Katz ya kuma ce yuwuwar nasarar kisan gillar da gwamnati ta yi kan al-Houthi zai iya tunawa da kisan gillar da Tel Aviv ta yi wa tsohon babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah, da kuma kisan Ismail Haniyeh, wanda shi ne shugaban ofishin siyasa na Hamas da Yahya Sinwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa
  • Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar
  • Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?
  • Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya
  • Isra’ila ta yi barazanar kashe shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen
  • Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
  • Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa