Aminiya:
2025-11-03@03:09:29 GMT

Mataimakiyar shugaban majalisar dokokin Edo ta yi murabus

Published: 19th, May 2025 GMT

Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Edo, Misis Maria Oligbi-Edeko, ta ajiye muƙaminta.

Ta bayyana murabus ɗinta ne a zaman majalisar da aka yi a ranar Litinin a Birnin Benin, babban birnin jihar.

Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200

Oligbi-Edeko, wadda ke wakiltar mazaɓar Esan ta Arewa Maso Gabas II, ta ce ta yi murabus ne, saboda jam’iyyarta ta PDP ta rasa rinjaye a majalisar bayan wasu ’yan jam’iyyar ciki har da Shugaban Majalisar sun koma jam’iyyar APC.

An zaɓe ta a matsayin Mataimakiyar Shugaban Majalisar karo na takwas a ranar 16 ga watan Yunin 2023, kafin ta yi murabus.

Bayan ta yi murabus, majalisar ta zaɓi Mista Osamwonyi Atu daga jam’iyyar APC (Orhionmwon ta Gabas) a matsayin sabon mataimakin shugaban majalisar.

Jagoran Majalisar, Hon. Jonathan Aigbokhan, ya gabatar da ƙuduri cewa a ci gaba da biyanta dukkanin haƙƙoƙinta da ke tattare da kujerar mataimakiyar shugaban majalisar.

Wannan ƙuduri ya samu goyon bayan shugaban ’yan adawa, Hon. Charity Airobarueghian, kuma dukkanin ‘yan majalisar sun amince da shi.

A cikin wasiƙar murabus ɗinta, Oligbi-Edeko ta ce ta yi hakan ne domin tabbatar da adalci, gaskiya da daidaito ga dukkanin mazaɓu.

Ta kuma gode wa shugabanni da mambobin jam’iyyar PDP saboda damar da suka bata ta wakilci mazaɓarta.

’Yan majalisar sun yaba da ƙoƙarinta da jajircewarta wajen yi wa jama’a hidima.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Mataimakiyar Shugaban Majalisa Murabus Siyasa shugaban majalisar ta yi murabus

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike

Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.

Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

Sauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.

An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.

Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.

Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.

Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa