Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
Published: 24th, April 2025 GMT
An garzaya da ita asibitin Misau, daga nan aka mayar da ita zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Azare, inda aka tabbatar da mutuwarta.
Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi, CSP Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis.
Ya ce waɗanda aka kama sun amsa laifin kuma sun bayyana sunayen wasu da suka haɗa kai da su.
Cikin sauran waɗanda aka kama har da Alkali Kawu, Maule Mai Ride, Mai Tumatir, Danguli, Yakubu da Kura.
Wakil ya ce bincike yana guduna a hedikwatar ‘yansanda ta Misau, kuma sun ƙudiri aniyar ganin adalci ya tabbata.
Ya ƙara da cewa bayan kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu domin fuskantar hukunci daidai da laifin da suka aikata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yansanda Budurwa Fyaɗe Zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Makama Hardawa, ya rasu.
Marigayin ya rasu ne ranar Talata a Abuja, bayan ya yi fama da gajeruwar jinya.
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ne ya tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa ranar Laraba.
Muna tafe da karin bayani…