An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
Published: 24th, April 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta kama wasu mata biyu a lokacin da suke yunƙurin sayar da wani yaro ɗan shekara huɗu da aka yi garkuwa da shi a Owerri kan kuɗi Naira miliyan 2.7.
An yi garkuwa da yaron ne a Abuja a lokacin da yake tallan kayan miya, sannan aka kawo shi Owerri a sayar da shi kafin a sa’ar kuɓutar da shi daga masu son sayar da shi.
Waɗanda ake zargin sun haɗa da Joy Ugwu daga garin Idah ta jihar Kogi, da Rosella Michael daga garin Zamba da ke Abuja, yayin da ta ukun da ake zargin ma’aikaciyar jinya ce da ta tsere a yanzu.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Henry Okoye ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.
Okoye ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a Owerri, babban birnin jihar a ranar 14 ga watan Afrilu, biyo bayan wani samame da jami’an tsaro suka yi a lokacin da suke ƙoƙarin siyar da yaron kan kuɗi Naira miliyan 2.7.
Ya ce, an kama mutanen ne biyo bayan ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin rundunar ’yan sandan Jihar Imo da hedikwatar ’yan sandan shiyya ta 7 da ke Abuja, duk da cewa an miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na shiyyar Abuja, domin ci gaba da bincike da gurfanar da su gaban kuliya.
Okoye ya ce, “Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta gano wani mutum da ake zargi da safarar ƙananan yara, lamarin da ya kai ga cafke wasu mata biyu da ake zargi tare da kuɓutar da wani yaro ɗan shekara huɗu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Owerri da ake zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
Aƙalla mutum 26 ne suka rasu sakamakon wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka a Jihar Binuwai.
Hare-haren sun faru ne a yankunan Ƙaramar Hukumar Makurdi da Katsina-Ala tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na daren ranar Alhamis.
Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasuA Ƙaramar Hukumar Makurdi, wasu ’yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Mtswenem da Akondotyough Bawa, inda suka kashe mutum 25.
Haka kuma, an kashe mutum ɗaya a wani hari daban da aka kai ƙauyukan Kenvanger da Agbami a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala.
Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun shiga gidajen mutane suna harbin su yayin da suke barci, suna amfani da bindigogi da adduna.
Wani wanda ya tsira mai suna Iorpuu, ya ce mata da yara suna cikin waɗanda aka kashe, kuma har yanzu ana neman wasu da suka ɓace.
Ya ƙara da cewa wasu sun mutu ne a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.
Wani ganau ya ce an fara kai harin ne wani ƙauye kusa da Jami’ar Noma da Fasaha ta Makurdi, inda aka kashe mutane huɗu.
Daga nan suka wuce wani ƙauye a kusa da unguwar Low Cost suka ci gaba da kashe mutane har adadin gawarwakin ya kai 25.
A Katsina-Ala, ’yan bindigar sun kai hari ƙauyukan Kenvanger da Agbami da misalin ƙarfe 1 na dare.
An ce sun yi yunƙurin yi wa wasu matan da suka haihu fyaɗe, amma mazan ƙauyen suka kai musu ɗauki.
Wannan ya haifar da rikici inda ’yan bindigar suka buɗe wuta, suka kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu.
A ƙauyen Agbami kuma, sun yi wa mutane da yawa dukan kawo wuƙa amma babu wanda ya mutu.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ya tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru a Makurdi.
Ya ce za su ci gaba da bai wa ’yan jarida bayanai, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani.