HausaTv:
2025-07-31@02:03:56 GMT

Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI

Published: 20th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da barazanar HKI na kaiwa cibiyoyin makamashin nukliyar kasar don hana kasar abinda take kira makaman Nukliya.

Ministan ya kara da cewa kasar Iran zata iya kare kanta ko da Amurka ce ta takaleta, kuma Amurka ta san hakan. Sannan ya ce HKI bata taba kaiwa Iran hari a bay aba kuma ba zata taba kai mata hari ba.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya buga wannan labarin a jiya Asabar ya kuma nakalto ministan yana cewa kasashen Rasha da Iran basu taba karfafa dangantakar tsakaninsu fiye da yanzu ba.

Aragchi ya kara da cewa kasashen Iran Rasha da kuma China suna aiki tare don tabbatar da zaman lafiya a duniya a cikin yan shekarun da suka gabata. Kuma kasashen da gaske suke a kan hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya

Wani jami’in kasar Ukiraniya ya bayyana cewa, a kalla mutane 8 ne su ka jikkata sanadiyyar munanan hare-haren da Rasha ta kai wa birnin Kiev ta hanyar amfani da makamai masu linzami.

Shugaban sha’anin tafiyar da Mulki na soja a birnin Kiev Taimur Tikatishinko ya wallafa sanarwa a shafinsa na “Telegram’ cewa; A tsakanin wadanda su ka jikkata din da akwai karamin yaro dan shekaru 3, kuma tuni an dauki mutane 4 zuwa asibiti, daya daga cikinsu yana cikin mummunan hali.

Shi kuwa magajin birnin na Kiev Fitali Kikitshiko cewa ya yi, mutanen da su ka jikkata suna zaune ne a cikin gidaje mabanbanta a unguwa daya.

Har ila yau ya kara da cea; Harin ya haddasa fashewa mai karfi wacce ta sa tagogin gidaje su ka fashe, har zuwa gine-gine masu hawa 11.

A wani labarin daga jami’an kasar ta Ukiraniya, Rasha ta kai wasu hare-haren da jirage marasa matuki a garin Kirofifitsky wanda ya haddasa fashewa mai yawa.

A cikin makwannin bayan nan dai Rasha ta tsananta kai hare-hare a fadin kasar  Ukiraniya ta hanyar amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuki.

Tun a 2022 ne dai Rasha ta fara kai wa Ukiraniya hare-hare bisa dalilin cewa tana son shiga cikin kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato.

Kasar ta Ukiraniya dai tana samun taimakon makamai da bayanai na sirri daga kungiyar ta Nato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ