Aminiya:
2025-11-03@02:59:53 GMT

Putin ya umarci tsagaita wuta a Ukraine albarkacin bikin Ista

Published: 20th, April 2025 GMT

Shugaba Vladimir Putin a yau Asabar ya umarci sojojin Rasha da su tsagaita buɗe wuta a Ukraine a wanan ranar ta Ista da kuma gobe Lahadi.

Putin ya kuma yi kira ga Kyiv da ta yi hakan, yayin da ake ganin tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura.

Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?

Haka kuma, Rasha da Ukraine sun yi musayar fursunonin yaƙi na sama da mutum 500 — kuma mafi girma tun bayan fara yaƙi a tsakanin kasashen biyu.

Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelenskiy, ya ce ƙasarsa ta karɓi sojoji fursunonin yaƙi akalla 277 waɗanda ke tsare a gidajen yarin Rasha, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Telegram.

Ita ma ma’aikatar tsaron Rasha ta ce ta karɓi sojojinta 246 daga Kiev, waɗanda a halin yanzu ke ƙasar Belarus wacce ke kawance da Rasha kafin daga bisani a maida su gida.

Kazalika, hukumomin Moscow da Kiev sun jinjina wa UAE wajen gudanar da wannan gagarumin aiki cikin kwanciyar hankali.

Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa dai ce ta shiga tsakani wajen ganin an yi musayar fursunonin cikin nasara tsakanin ƙasashen biyu da suka shafe shekaru uku suna gwabza yaƙi.

Bayanai sun ce Rasha ta kuma yi iƙirarin cewa ta kusan ƙwato yankunan da sojojin Ukraine suka mamaye tun lokacin bazarar shekara ta 2024 a yankin Kursk da ke kan iyakar Rasha.

Ƙasashen duniya na ci gaba da kira na ganin an kawo ƙarshen wannan yaƙi, duk da cewa Rashan da Ukraine kowanensu na iƙirarin samun galaba a yaƙin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta

Bayan duguwar tattaunawa a birnin Istanbul na kasar turkiya kasashen pakisatan da Afghanistan sun amince da batun tsawaita dakatar da bude wuta a tsakanin iyakokin kasashen,  bayan da kasashen turkiya da Qatar suka shiga tsakanin domin samun daidaito.

Gwabzawa a iyakokin kasashen biyu dake mukwabtaka a yan makwannin nan yana barazana sosai ga zaman lafiyar yankin, sai dai wannan yarjejeniyar za ta hana yaduwar fadan da kuma kara samun hadin guiwa kan tsaron iyakokin.

Zabiullah mujahid kakakin kungiyar Taliban ya tabbatar da kulla yarjejeniyar, kuma yace Kabul tana son samun kyakkyawar dangantaa da dukkan kasashen dake makwabtaka da ita, musamman kasar Pakistan bisa mutunta juna da kuma rashin tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashen.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari