Aminiya:
2025-06-15@06:28:07 GMT

Harajin China da Amurka: Mene ne makomar tattalin arziƙin duniya?

Published: 9th, April 2025 GMT

Sabon rikici ya sake kunno kai tsakanin ƙasashen China da Amurka, yayin da shugaba Donald Trump, ya ƙara wa kayayyakin da ake shiga da su ƙasar daga China haraji zuwa kashi 104.

Wannan matakin ya shafi kayayyaki kamar wayoyin hannu, batir, kayan wasan yara da na’urorin wasanni.

Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — Gwamnati  Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya China ta ce ba za ta zuba ido ba

China ta bayyana cewa ba za ta zuba ido ta yi tagumi yayin da ake gallaza mata.

China ta mayar da martani da nata harajin kashi wanda ta ƙada zuwa kashi 34 kan kayayyakin Amurka, inda ta kuma ce tana shirin ƙara wani harajin.

Ta rage darajar kuɗinta (Yuan) domin ƙarfafa fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.

A lokaci guda kuma, ta fara bincike kan wasu manyan kamfanonin Amurka kamar Google, inda kuma ta ke shirin daƙile wasu muhimman albarkatu.

Masana tattalin arziƙi na gargaɗin cewa wannan rikici zai shafi ƙasashe da dama, musamman na nahiyar Asiya kamar Vietnam da Cambodia, waɗanda harajin zai shafa daga Amurka.

Ana kuma ganin cewa wannan zai iya janyo hauhawar farashin kayayyaki a Amurka da kuma raguwar sayayya daga China.

Wannan ba rikicin haraji ba ne – Ƙwararru

Wasu ƙwararru sun bayyana cewa wannan ba kawai rikicin haraji ba ne, wata gwagwarmaya ce ta nuna iko a harkokin kasuwancin duniya.

Ko da yake tattalin arziƙin China na fuskantar tangarɗa a yanzu, amma masana na ganin tana iya ɗorewa, domin kauce wa nuna rauni ga matakin da Amurka ke kai mata.

A gefe guda kuwa, Amurka na fama da matsin lamba daga ‘yan kasuwa da masu zuba jari da ke jin tsoron sakamakon wannan rikici.

Masana na fargabar lokacin da rikicin zai ƙare

Masana sun bayyana cewa da wuya a san yadda wannan rikici zai ƙare.

Amma ana fatan cewa shugabannin ƙasashen biyu za su zauna tattaunawa domin samun mafita.

Ƙasashen duniya na fargabar cewa idan ba a daidaita ba, rikicin na iya taɓa tattalin arzikin duniya gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: duniya Haraji Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda ya tattauna ta wayar tarho da jami’ar harkokin waje ta tarayyar turai ya bayyana cewa, ci gaba da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ba shi da wata ma’ana, kamata ya yi jami’an tarayyar turai din su yi Allawadai da wuce gona da irin HKI akan Iran.

Da safiyar yau Asabar ne dai jami’ar diplomasiyyar ta turai Kaja Kallas ta kira yi minsitan harkokin wajen jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci inda su ka tattauna halin da ake ciki a yammacin Asiya da ya hada da harin da HKI ta kawo wa Iran.

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana harin na HKI da cewa, wuce gona da iri ne da keta hurumin kasar Iran, kuma harin da ta kai wa cibiyoyin Nukiliya ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da su ka hada da malaman jami’oi , da kuma mata da kananan yara.

Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi Allawadai da abinda HKI ta yi na take dokokin kasa da kasa.

Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran ya yi ishara da cewa, kudurin da majalisar alkalai ta hukumar makamashin Nukiliyar Iran ta fitar akan Iran wanda kuma kasashe uku na turai tare da Amurka su ka gabatar da shi, shi ne ya bude wa ‘yan Sahayoniya mashigar da su ka yi amfani da ita wajen wuce gona da iri akan Iran.

A nata gefen babbar jami’ar diplomasiyyar tarayyar turai ta bayyana rashin jin dadinta akan abinda yake faruwa a cikin yankin na yammacin Asiya na rikice-rikice, tare da bayyana cewa suna goyon bayan aiki da diplomasiyya domin tabbatar da zaman lafiya.

A wani labarin mai alaka da wannan kasar Oman ta sanar da cewa, ba za a yi taron da aka shirya yi a tsakanin Iran da Amruka ba.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ce ta fitar da sanarwar cewa; Tattaunawar da aka shirya cewa za a yi a tsakanin Amurka da Iran ba za a yi ta ba a gobe Lahadi.

Ministan harkokin wajen na Oman ya kara da cewa; Diplomasiyya ce kadai ya kamata ta zama hanyar cimma zaman lafiya mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122