Aminiya:
2025-04-30@23:18:08 GMT

’Yan bindiga sun mamaye garuruwa 64 a Filato — Gwamna Mutfwang

Published: 9th, April 2025 GMT

Gwamna Caleb Mutfwang ya bayyana damuwa kan yadda matsalar tsaro ta ƙara ƙamari, yana mai cewa a halin yanzu ’yan bindiga sun mamaye aƙalla garuruwa 64 na Jihar Filato.

A wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a yau Laraba, Gwamna Mutfwang ya ɗora alhakin matsalar tsaron da ake fuskanta a jiharsa kacokam a kan ta’addancin ’yan bindiga da ke ƙara ta’azzara.

Ibas ya naɗa kantomomin ƙananan hukumomin Ribas ’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a Sakkwato

Gwamnan ya yi zargin cewa akwai masu ɗaukar nauyin hare-haren da ke aukuwa a jiharsa.

“A haƙiƙanin gaskiya babu wani bayani da zan yi face cewa akwai masu ɗaukar nauyin ta’addancin nan,” a cewar gwamnan.

“Abin tambayar shi ne, su wa ke ɗaukar nauyin ta’addancin? Wannan shi ne abin da hukumomin tsaro za su yi ƙoƙari su gano.

“Mun zo gaɓar da za a gano masu hannu a wannan lamari domin dole akwai masu ɗaukar nauyin waɗannan hare-haren.

“Waɗannan garuruwa da a bayan nan aka kai wa hari suna cikin yankunan da suka fuskanci hare-hare a 2023 amma suka sake gina alaƙaryar da kansu.

“Misali, a shekarar 2023 an kai wa ƙauyen Ruwi hari har aka kashe mutane 17, amma suka sake farfaɗowa suka gina matsugunninsu.

“Idan an ɗauki kusan shekaru 10 ana wannan hare-hare, shi yake nuna cewa akwai wasu da ke shirya wannan ta’addanci da gayya domin kawar da mutane daga doron ƙasa.

“A halin yanzu akwai aƙalla garuruwa 64 da ’yan bindiga suka mamaye a tsakanin ƙananan hukumomin Bokkos, Barkin Ladi, da Riyom na Jihar Filato.

“’Yan bindiga sun ƙwace iko waɗannan wurare sun sauya musu suna kuma mutane sun ci gaba da rayuwa a cikinsu.

“Sai dai ina fatan cewa nan da wani lokaci kaɗan hukumomin tsaro za su haɗa gwiwa domin kawo ƙarshen wannan matsalar.

Aminiya ta ruwaito cewa a makon jiya ne Gwamna Mutfwang ya yi iƙirarin cewa matsalar tsaron da ke addabar jihar ta wuce iya rikicin makiyaya da manoma.

“Dole ne na nanata cewa manufar waɗannan maƙiya ita ce tayar da hargitsi da hana zaman lafiya a jihar nan.

“Sai dai ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba har sai mun tabbatar da cewa burinsu bai cika ba.

“Masu tunanin cewa rikicin makiyaya da manoma ne ka haddasa matsalar tsaro su daina wannan tunani domin kuwa wasu ne ke sojan gona da zummar hana zaman lafiya a jihar.

“Ina mai tabbatar wa mutanen Filato cewa da izinin Allah za mu yi nasara a kansu kuma mun kusa ganin ƙarshen waɗannan maƙiya,” a cewar gwamnan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Caleb Muftwang hare hare Jihar Filato ɗaukar nauyin matsalar tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.

Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.

Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.

“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.

“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.

“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114