Aminiya:
2025-06-15@08:22:31 GMT

’Yan bindiga sun mamaye garuruwa 64 a Filato — Gwamna Mutfwang

Published: 9th, April 2025 GMT

Gwamna Caleb Mutfwang ya bayyana damuwa kan yadda matsalar tsaro ta ƙara ƙamari, yana mai cewa a halin yanzu ’yan bindiga sun mamaye aƙalla garuruwa 64 na Jihar Filato.

A wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a yau Laraba, Gwamna Mutfwang ya ɗora alhakin matsalar tsaron da ake fuskanta a jiharsa kacokam a kan ta’addancin ’yan bindiga da ke ƙara ta’azzara.

Ibas ya naɗa kantomomin ƙananan hukumomin Ribas ’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a Sakkwato

Gwamnan ya yi zargin cewa akwai masu ɗaukar nauyin hare-haren da ke aukuwa a jiharsa.

“A haƙiƙanin gaskiya babu wani bayani da zan yi face cewa akwai masu ɗaukar nauyin ta’addancin nan,” a cewar gwamnan.

“Abin tambayar shi ne, su wa ke ɗaukar nauyin ta’addancin? Wannan shi ne abin da hukumomin tsaro za su yi ƙoƙari su gano.

“Mun zo gaɓar da za a gano masu hannu a wannan lamari domin dole akwai masu ɗaukar nauyin waɗannan hare-haren.

“Waɗannan garuruwa da a bayan nan aka kai wa hari suna cikin yankunan da suka fuskanci hare-hare a 2023 amma suka sake gina alaƙaryar da kansu.

“Misali, a shekarar 2023 an kai wa ƙauyen Ruwi hari har aka kashe mutane 17, amma suka sake farfaɗowa suka gina matsugunninsu.

“Idan an ɗauki kusan shekaru 10 ana wannan hare-hare, shi yake nuna cewa akwai wasu da ke shirya wannan ta’addanci da gayya domin kawar da mutane daga doron ƙasa.

“A halin yanzu akwai aƙalla garuruwa 64 da ’yan bindiga suka mamaye a tsakanin ƙananan hukumomin Bokkos, Barkin Ladi, da Riyom na Jihar Filato.

“’Yan bindiga sun ƙwace iko waɗannan wurare sun sauya musu suna kuma mutane sun ci gaba da rayuwa a cikinsu.

“Sai dai ina fatan cewa nan da wani lokaci kaɗan hukumomin tsaro za su haɗa gwiwa domin kawo ƙarshen wannan matsalar.

Aminiya ta ruwaito cewa a makon jiya ne Gwamna Mutfwang ya yi iƙirarin cewa matsalar tsaron da ke addabar jihar ta wuce iya rikicin makiyaya da manoma.

“Dole ne na nanata cewa manufar waɗannan maƙiya ita ce tayar da hargitsi da hana zaman lafiya a jihar nan.

“Sai dai ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba har sai mun tabbatar da cewa burinsu bai cika ba.

“Masu tunanin cewa rikicin makiyaya da manoma ne ka haddasa matsalar tsaro su daina wannan tunani domin kuwa wasu ne ke sojan gona da zummar hana zaman lafiya a jihar.

“Ina mai tabbatar wa mutanen Filato cewa da izinin Allah za mu yi nasara a kansu kuma mun kusa ganin ƙarshen waɗannan maƙiya,” a cewar gwamnan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Caleb Muftwang hare hare Jihar Filato ɗaukar nauyin matsalar tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa

A ranar dimokuraɗiyyar Najeriya ta 2025, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Alhamis, ya yi afuwa ga fursunoni 66 a babbar Cibiyar gyaran hali da ke Maiduguri.

Ziyarar da Gwamna Zulum ya kai a gidan yari a ranar 12 ga watan Yuni, 2025, ya yi amfani da ikon da sashe na 212 na kundin tsarin mulkin Najeriya ya ba wa gwamnonin jihohi, wanda ya ba da damar yin afuwa bayan ya tattauna da wata majalisar ba da shawara kan jinƙai.

12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe

“Dangane da ikon da aka bani a ƙarƙashin sashe na 212 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya (wanda aka gyara) da kuma shawarwarin kwamitin bayar da shawara kan jinƙai, don haka na yi afuwa ga fursunoni 66 da ke babbar cibiyar gyaran hali da ke nan Maiduguri,” in ji Zulum.

Ya kuma ƙara da cewa “Na kuma mayar da hukuncin kisa zuwa ɗaurin rai-da-rai tare da rage wa wasu fursunoni hukuncin zaman gidan yari a wani ɓangare na bukukuwan murnar zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya ta bana.”

“Bayan afuwar, Gwamna Zulum ya yi wani gagarumin tallafi ta hanyar ba da gudummawar tsabar kuɗi Naira dubu 20 ga kowanne fursunoni 1,280 da ke cikin wannan gidan gyaran.”

Don ci gaba da gudanar da bukukuwan ranar dimokraɗiyya a cibiyar, ya kuma sanar da bayar da gudummawar buhunan shinkafa 300, galan 50 na man girki, da shanu guda 5.

Da yake mayar da jawabi Kwanturolan gidan gyaran hali na jihar Borno, Ibrahim Bawa ya yaba da ziyarar da Gwamnan ya kai wanda ya ce ba a taɓa yin irinsa ba.

“Wannan shi ne irinsa na farko,” in ji shi.

Yana mai cewa, babu wani gwamnan da ya gabata da ya ziyarci wurin domin yin murna ga fursunonin, musamman waɗanda suka yi sa’ar shaƙar iskar ’yanci.

Bawa ya kuma tuno da irin karamcin da Gwamnan ya yi a baya da suka haɗa da kyaututtukan buhunan shinkafa 100, galan-gadan na man girki 25, da bijimai 10 a lokacin bikin Sallah na Eid-el-Kabir na baya, wanda ya ce duk fursunoni da ma’aikata sun ji daɗin su.

Mista Gambo Samuel, wanda aka fi sani da Sarkin Gida, kuma shugaban fursunonin, ya nuna matuƙar godiya ga Gwamna Zulum dangane da wannan alfarma da ya musu na afuwar da kuma kayan abincin da ya kawo musu tallafinsa.

Ya kuma yaba wa ƙoƙarin Gwamnan na kawo sauyi a faɗin jihar, wanda ya lura akai-akai ana jin labarin sa daga sabbin fursunonin da ke shigowa wannan cibiyar lokaci zuwa lokaci.

Baya ga ziyarar da ya kai gidan gyaran halin, Gwamna Zulum ya kuma ƙaddamar da wasu ayyukan raya    ƙasa da dama na tunawa da ranar dimokuraɗiyya a cikin birnin Maiduguri da suka shafi hanyoyin mota, ruwan sha, cibiyoyin kiwon lafiya da makamantansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato