Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ci gaba da gudanar da  tarurrukan bita ga maniyyata aikin Hajjin bana, bayan  kammala azumin watan Ramadan.

Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, hukumar za ta tabbatar da cewa maniyyata sun sami horo da ilimi kan yadda ake aiwatar da aikin Hajji domin dacewa wannan ibada da suka kashe makudan kudade don gannin sun aiwatar da ita.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, za a wayar da kan alhazai da kuma koya musu yadda za su kula da kansu da kuma yadda za su aiwatar da aikin Hajji bisa ga koyarwar addini.

Ya ce, ana gudanar da wannan taron bitar ne a kullum, a cibiyoyi 27 da aka ware a fadin jihar.

Haka kuma, ya ce, taron bitar zai  taimakawa Alhazan wajen fahimtar dokoki da sabbin tsare-tsaren da hukumomin Saudiyya da hukumar Hajji ta kasa NAHCON suka tsara domin aikin Hajjin shekarar 2025.

Labbo ya yi kira ga dukkanin alhazan bana da su rika halartar wadannan tarurruka domin sanin abubuwan da suka dace.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma yaba maniyyatan bisa yadda suke daukar wannan taron koyarwa da muhimmanci.

Daraktan ya kuma shawarce su da su ci gaba da nuna dabi’un kirki kamar yadda suka saba, tare da zama jakadu nagari ga jihar, da kasa baki daya, tare da bin doka da oda a masarautar Saudiyya.

Ya ce, hukumar ta riga ta tanadi masauki mai tsafta kusa da Masallacin Harami ga alhazan jihar, tare da shirya yadda za a rika ba su abinci ta hannun wani kamfani na kasar Saudiyya.

Labbo ya kuma yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da hadin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Taron Bita

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya sanya wa sabuwar gadar sama da aka kammala a Lafia, Babban Birnin Jihar, sunan Shugaba Bola Tinubu.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ƙaddamar da aikin a Lafia.

’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano

Ya ce an gina gadar bisa tsarin Shugaba Tinubu, kuma an kammala aikin ne ba tare da ciyo bashi ba, sakamakon inganta amfani da kuɗin gwamnati.

Sabuwar gadar mai tsawon kilomita ɗaya, wadda ke da gadar sama da ƙasa, na ɗauke da sunan ‘Bola Tinubu Exchange Road’.

A wajen buɗe aikin, Shugaba Tinubu ya gode wa Gwamna Sule bisa jajircewarsa wajen aiwatar da ayyukan da ke taimaka wa rayuwar al’umma.

Haka kuma, ya nuna farin cikinsa da irin tarbar da ya samu daga mutanen Nasarawa.

Sannan ya yi kira a gare su da su ci gaba da mara wa gwamnati baya wajen bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
  • Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin