Aminiya:
2025-05-23@22:45:21 GMT

Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah

Published: 30th, March 2025 GMT

Ranar idin Karamar Sallah rana ce da Musulmi ke farin cikin kammala azumin watan Ramadan wacce ke zuwa a ranar daya ga watan Shawwal din shekarar Musulunci.

Allah Madaukakin Sarki ya shar’anta Sallar Idi a matsayin ibadar kammala Azumin Ramadan wacce take kan kowane Musulumi, baligi, mai hankali, kuma mazaunin gida —  namiji ko mace.

Zakatul Fidr: Yadda ake fitar da Zakkar Kono Zakkar Fidda Kai ta fi kayan sallah da abincin sallah

A yayin da ake shirin shan shagalin Kamar Sallah, malamai sun bayyana muhimman abubuwan da ya kamata su aikata a ranar, kamar yadda Hadisan Annabi (SAW) suka nuna:

Duk Musulumi maza da mata manya da kanana su halarci sallar Idi. Fitar da zakkar fid da kai, wato Zakkar Kono. Cin dabino ko abinci kafin zuwa Sallar Idi. Yin wankan idi kafin zuwa halartar sallar idi. Sanya sabbi ko mafiya kyawtun tufafi da mutum ya mallaka. Sanya turare da yanke farce Ana son sanya turare ga maza. Yawaitawa da kuma bayyana kabarbari ga maza da mata. Daina yin kabbarori daga lokacin da aka tayar da sallar.
Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, LaiLaha illAllah, Allahu Akbar walillahil hamdu. Sauraron huduba bayan kammala Sallar. Zuwa sallar da dawowa ta hanyoyi daban-daban. Rashin zuwa da makami ko wani abu da zai razana mutane sallar idi. Ziyara da taya ’yan uwa da sauran murna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sallar Idi zakkar fidda kai Allahu Akbar

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC

Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta sanya ranar 3 ga watan Yuni, 2025 domin yanke hukunci kan shari’ar BBC da mawaƙi Abdul Kamal.

Tunda farko Abdul, ya maka kafar ne a kotu, inda yake neman ta biya shi diyyar Naira miliyan 120, kan zargin amfani da waƙarsa a shirinsu na “Daga bakin mai ita” ba tare da izininsa ba.

Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum

A zaman shari’ar na ranar Litinin, lauyan mai ƙara, Barista Bashir Ibrahim Umar, ya gabatar da makaɗin waƙar, Muhammad Sani Uba a matsayin ɗaya daga cikin shaidun wanda ke ƙara.

Makaɗin ya tabbatar wa kotu cewa shi ne, ya yi wa Kamal kiɗan da ake shari’ar a kansa.

Daga bisani alƙalin kotun, ya sanya ranar 3 ga watan Yuni, 2025 domin yanke hukunci kan shari’ar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
  • Tinubu Zai Bibiyi Kwazon Ministocinsa A Ranar 29 Ga Watan Mayu
  • Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya
  • Jami’ar Ilorin Ta Yi Bikin Ranar Al’adu
  • Kamfanonin jiragen sama sun tsawaita dakatar da zirga-zirgar zuwa Isra’ila
  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
  • Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya