Aminiya:
2025-11-03@03:01:17 GMT

Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah

Published: 30th, March 2025 GMT

Ranar idin Karamar Sallah rana ce da Musulmi ke farin cikin kammala azumin watan Ramadan wacce ke zuwa a ranar daya ga watan Shawwal din shekarar Musulunci.

Allah Madaukakin Sarki ya shar’anta Sallar Idi a matsayin ibadar kammala Azumin Ramadan wacce take kan kowane Musulumi, baligi, mai hankali, kuma mazaunin gida —  namiji ko mace.

Zakatul Fidr: Yadda ake fitar da Zakkar Kono Zakkar Fidda Kai ta fi kayan sallah da abincin sallah

A yayin da ake shirin shan shagalin Kamar Sallah, malamai sun bayyana muhimman abubuwan da ya kamata su aikata a ranar, kamar yadda Hadisan Annabi (SAW) suka nuna:

Duk Musulumi maza da mata manya da kanana su halarci sallar Idi. Fitar da zakkar fid da kai, wato Zakkar Kono. Cin dabino ko abinci kafin zuwa Sallar Idi. Yin wankan idi kafin zuwa halartar sallar idi. Sanya sabbi ko mafiya kyawtun tufafi da mutum ya mallaka. Sanya turare da yanke farce Ana son sanya turare ga maza. Yawaitawa da kuma bayyana kabarbari ga maza da mata. Daina yin kabbarori daga lokacin da aka tayar da sallar.
Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, LaiLaha illAllah, Allahu Akbar walillahil hamdu. Sauraron huduba bayan kammala Sallar. Zuwa sallar da dawowa ta hanyoyi daban-daban. Rashin zuwa da makami ko wani abu da zai razana mutane sallar idi. Ziyara da taya ’yan uwa da sauran murna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sallar Idi zakkar fidda kai Allahu Akbar

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure

Babbar Kotun Kano mai lamba 7 da ke zama a cikin birni ta bayar da umarnin tsare Aminu Ismail, mazaunin Unguwar Bai a Karamar Hukumar Ajingi ta jihar, bisa zarginsa da kashe mahaifinsa, Malam Dahiru Ahmad, ta hanyar caka masa wuƙa har lahira.

Lamarin ya faru ne bayan samun sabani tsakaninsu kan aniyar Aminu ta ƙara aure, wadda mahaifinsa ya ƙi goyon baya saboda abin da ya kira halin tattalin arzikin da ake fama da shi a kasa.

Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

A cewar lauyan masu ƙara, Barrista Lamido Abba Sorondinki, wanda ake tuhuma ya shaida wa mahaifinsa niyyarsa ta kara mata ta biyu, amma mahaifinsa ya ba shi shawarar kada ya yi hakan, yana mai danganta matsalar da halin tattalin arzikin ƙasa ke ciki.

Wannan sabani ya rikide zuwa faɗa, inda ake zargin Aminu da caccaka wa mahaifin nasa wuƙa a ƙirji, lamarin da ya jawo masa rauni mai tsanani har ya rasa ransa.

An gurfanar da Aminu da laifin kisan kai, wanda ya saba da Sashe na 221 na kundin penal code.

Ana ci gaba da shari’ar, kuma kotu ta bayar da umarnin tsare shi har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraron ƙarar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure