Leadership News Hausa:
2025-07-30@11:52:13 GMT

Yaushe Ronaldo Zai Daina Jefa Kwallo A Raga?

Published: 24th, March 2025 GMT

Yaushe Ronaldo Zai Daina Jefa Kwallo A Raga?

Cristiano Ronaldo ya zura ƙwallo a wasan da Portugal ta doke abokiyar karawarta ƙasar Denmark a daren ranar Lahadi, ƙwallon ita ce ta 929 da tsohon ɗan wasan na Manchester United ya jefa a tarihinsa na ƙwallon ƙafa, duk da cewar ya ɓarar da bugun daga kai sai mai tsaron gida a wasan da Portugal ta tsallake rijiya da baya, hakan ya sa ta kai wasan dab da na kusa da na karshe a gasar ta Nations League.

An tashi wasan ne da ci 3-3 jimilla bayan mintuna 90, amma Francisco Trincao ya sake zura kwallo a minti na 10 na ƙarin lokaci bayan da mai tsaron ragar Denmark Kasper Schmeichel ya ture wata ƙwallon da Goncalo Ramos ya buga.

Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi Ballon D’or: An Zaɓe Ni Ne Kamar Yadda Aka Zaɓe Ka – Martanin Rodri Ga Ronaldo

Goncalo Ramos wanda ya maye gurbin Cristino Ronaldo ne ya jefa ƙwallo ta biyar a ragar Denmark gab da za a tashi daga wasan, a wasan farko da ƙasashen su ka buga a ranar Alhamis, Denmark ce ta doke Portugal da ci ɗaya mai ban haushi.

Kafin a tashi wasan dai an karrama ɗan wasan tsakiya na Manchester City Bernardo Silva da kyautar girmamawa kasancewarshi ɗan wasa na 8 a tarihin ƙasar Portugal, da ya buga wasanni 100 a tawagar ƙwallon ƙafa ta Portugal ta maza, tawagar Roberto Martinez za ta kara da Jamus a wasan gaba, bayan da tawagar Julian Nagelsmann ta doke Italiya da ci 5-4 a wasanni biyu da su ka buga.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimakawa nasarar ayyukan tsaro a yankin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo
  • Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
  • An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
  • Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu