Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta  Hamas ta yi Allawadai da Hare-haren Amurka da Birtaniya akan kasar Yemen

Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas ta fitar da bayani na yin tir da hare-haren da jiragen yakin Amurka da Birtaniya su ka kai wa Birnin San’aa a jiya Asabar da dare.

Ita ma kungiyar Jihadul-Islami ta fitar da bayani na yin Allawadai da Amurka saboda harin da ta kai wa Yemen din, tana mai bayyana abinda ta aikata da cewa abin kunya ne da nuna goyon bayan ga laifukan da HKI take aikatawa akan al’ummar wannan yankin.

Kungiyar Jiahdul-Islami ta kuma yi jinjina ga kasar Yemen saboda yadda su ka tabbatar da jarunta ta asali irin ta Larabawa da musulmi wajen nuna goyon bayan mutanen Gaza da al’ummar Falasdinu.

Kwamitin al’umma na goyon bayan gwgawarmayar al’ummar Falasdinu ya bayyana harin na Amurka da Birtaniya akan Yemen da cewa, nuna goyon bayan ne karara ga HKI.

Bayanin ya kuma ce; Maharan ba za su karya kashin bayan al’ummar Yemen  ba da suke tsayin daka wajen taya Falasdinawa fada da kalubalantar killace mutanen Gaza da HKI ta yi, bisa goyon bayan Amurka.

Ita kuma kungiyar “Harkatul-Mujahidin” ta yi kira ne ga  rayayyun al’ummu da ‘yan gwgawarmaya da su hada karfi da karfe domin  fuskantar wuce gona da irin ‘yan sahayoniya da Amurka, tare da kara da cewa; Babu abinda zai takawa  masu daga hancin  da girman kai, birki,sai karfi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Amurka da Birtaniya na goyon bayan

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza

Kasashen Larabawa da musulmi 8 ne suka gamu suka ki amincewa da shirin HKI na korar Falasdinawa da karfi daga Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran tanakalto ministocin harkokin kasashen waje na kasashen Saudia, Masar, Jordan, da UAE Pakisatan Turkey da kuma Qatar sun bada bayanin hadin giwa daga kasashen Saudiya kan cewa shirin HKI na bude Kofar Rafah ta fcewar Falasdinawa Kawai ba tare da shigowa ba, baa bin amincewa bane.

Bayanin ya kara da cewa, wannan shirin yana da hatsari, kuma shiri ne wanda zai hana kafuwar kasar Falasdinu idan har duk wanda ya fit aba zai sake shigowa ba.  

Jami’an diblomasiyyar sun bayyana cewa, shirin ya sabawadokokin kasa da kasa, kuma  barazana ce ga samuwar kasar Falasdinu nan gaba. Dama HKI ta dade tana neman damar korar Falasdinawa daga Gaza, har abada, don hana su kokarin kafa kasar Falasdinu a kasarsu da aka mamaye.

Kasashen 8 sun bukaci a kawo karshen hare-haren da sojojin HKI suke kaiwa kan yankuna Falasdinawa a Gaza, ta kyale kayakin agaji su shiga sannan su bada dama a sake gina yankin. Sun bukaci a sake maida gwamnatin Hamas a gaza saboda ta ci gaba a harkokin gudanarwa.

Daga karshe sun bayyana cewa a shirye suke yi aiki don aiwatar da kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2803.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabi Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Sheikh Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Lebanon Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye December 6, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda December 6, 2025 Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  •  Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya
  • Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta  Kama Olmert Da Livni
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela
  • Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran
  • Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI