Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta  Hamas ta yi Allawadai da Hare-haren Amurka da Birtaniya akan kasar Yemen

Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas ta fitar da bayani na yin tir da hare-haren da jiragen yakin Amurka da Birtaniya su ka kai wa Birnin San’aa a jiya Asabar da dare.

Ita ma kungiyar Jihadul-Islami ta fitar da bayani na yin Allawadai da Amurka saboda harin da ta kai wa Yemen din, tana mai bayyana abinda ta aikata da cewa abin kunya ne da nuna goyon bayan ga laifukan da HKI take aikatawa akan al’ummar wannan yankin.

Kungiyar Jiahdul-Islami ta kuma yi jinjina ga kasar Yemen saboda yadda su ka tabbatar da jarunta ta asali irin ta Larabawa da musulmi wajen nuna goyon bayan mutanen Gaza da al’ummar Falasdinu.

Kwamitin al’umma na goyon bayan gwgawarmayar al’ummar Falasdinu ya bayyana harin na Amurka da Birtaniya akan Yemen da cewa, nuna goyon bayan ne karara ga HKI.

Bayanin ya kuma ce; Maharan ba za su karya kashin bayan al’ummar Yemen  ba da suke tsayin daka wajen taya Falasdinawa fada da kalubalantar killace mutanen Gaza da HKI ta yi, bisa goyon bayan Amurka.

Ita kuma kungiyar “Harkatul-Mujahidin” ta yi kira ne ga  rayayyun al’ummu da ‘yan gwgawarmaya da su hada karfi da karfe domin  fuskantar wuce gona da irin ‘yan sahayoniya da Amurka, tare da kara da cewa; Babu abinda zai takawa  masu daga hancin  da girman kai, birki,sai karfi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Amurka da Birtaniya na goyon bayan

এছাড়াও পড়ুন:

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

A yau Laraba 5 ga watan Nuwamba, an bude bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin na kasa da kasa (CIIE) karo na 8 a birnin Shanghai. A yayin wani taron manema labarai na yau da kullum da ya gudana a wannan rana, mai magana yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta nuna cewa, nasarar karbar bakuncin bikin baje kolin CIIE tsawon shekaru takwas a jere ta nuna kudurin kasar Sin da ayyukanta na cika alkawarinta na bude kofa, da kuma cimma burin samun moriyar juna da kuma nasara ga kowane bangare.

Mao Ning ta bayyana cewa bikin baje kolin na CIIE shi ne babban baje kolin kayayyaki a matakin na kasa na farko a duniya wanda ke da jigon shigo da kayayyaki daga waje, kuma wani sabon salo ne da yunkuri mai alfanu ga kasar Sin don ta fadada bude kofa ga sauran kasashe.

Girman bajen kolin CIIE na wannan shekarar ya gawurta zuwa sabon matsayi, inda kamfanoni sama da 4100 daga kasashen waje suke halarta. Harka tare da kasar Sin tamkar mabudi ne na samun damammaki, wanda hakan ya samu ittifakin amincewa a tsakanin dukkan bangarorin da suke halarta. Kasar Sin za ta ci gaba da fadada bude kofa da kuma sanya babbar kasuwarta ta zamo babbar dama ga duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka November 5, 2025 Daga Birnin Sin Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin November 5, 2025 Daga Birnin Sin Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Shugaban Kasar Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi
  • Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba
  • Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na Amurka
  • Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
  • Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
  • “Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
  • Kungiyar Likitocin Kasar Sudan: Rundunar RSF Tana Garkuwa Da Dubban Fararen Hula A Al-Fasha
  • Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump