Aminiya:
2025-09-18@08:23:38 GMT

Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kaza

Published: 27th, February 2025 GMT

Wata kotun majistare da ke zamanta a Ago Iwoye, Jihar Ogun, ta yanke wa wani matashi ɗan shekara 21, Adebanjo Segun, hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari bisa samunsa da laifin satar kaza.

Jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar tsaro ta Civil Defence , Dyke Ogbonnaya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

An ce an fara samun matsalar ne a ranar Laraba, 19 ga Fabrairu, 2025, kan Adebanjo mai shekara 21 a lokacin da aka kama shi da laifin satar kaza.

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Ogbonnaya ya bayyana cewa, “Bayan an yi nazari sosai kan lamarin tare da kammala bincike, an gano cewa wanda ake tuhuma ya aikata irin wannan laifin a wani lokaci a watan Disambar 2024 inda aka yi masa afuwa a matsayin wanda ake zato da ya yi laifin farko.

“Saboda bayyana laifin da ya aikata a baya, an gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare ta Ago-Iwoye kan tuhume-tuhumen da ya shafi sashe na 430 na dokokin manyan laifuka na Jihar Ogun, Nijeriya 2006, a ranar 20 ga Fabrairu, 2025.

“Bayan ya amsa laifinsa a gaban Alƙali ​​O.F. Adeduntan, an same shi da laifin kuma  kotun ta yanke masa hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari.”

Hakazalika, an kuma yanke wa wani Kazeem Tobi mai shekara 20 hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari bisa samunsa da laifin satar janareta na Elepaƙ wanda kuɗinsa ya kai kusan N120,000 kacal.

An ce an sake gurfanar da Tobi a ranar Talata, 4 ga watan Fabrairu, 2025, kuma bayan da aka yi nazari sosai a kan lamarin, an gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare ta Ago-Iwoye kan tuhume-tuhume biyu da suka shafi haɗa baki wajen aikata laifi da kuma mallakar wani abu da ake zargin an sace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidan Yari satar kaza

এছাড়াও পড়ুন:

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sun jaddada cewa dole ne manyan kafafen sada zumunta su kare ‘yancin yin magana.

Sun kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, ‘yan jarida, da masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama su tashi tsaye don hana abin da suka kira yunƙurin mayar da Nijeriya “mulkin kama-karya a intanet.”

Lamarin ya biyo bayan wa’adin sati guda da DSS ta bai wa Sowore da ya goge wasu wasu rubuce-rubuce game da Shugaba Bola Tinubu, wanda ya ƙi amincewa.

Hakan ya sa hukumar ta shigar da shi ƙara a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata