Jam’iyyar NNPP a jihar Kano ta dakatar da wasu mambobinta da suka hada da Sanata da wasu ‘yan majalisar tarayya uku bisa zargin zagon kasa ga jam’iyyar.  Shugaban jam’iyyar NNPP na jihar, Alhaji Hashimu Dungurawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano ranar Litinin, inda ya bayyana rashin jin dadin jam’iyyar da halayyar ‘yan majalisar da aka dakatar.

NNPP Ta Dakatar da ‘Yan Majalisa Huɗu Bisa Zargin Yi Wa Jam’iyya Zagon Ƙasa Nan Kusa Ƴan Majalisun NNPP Za Su Koma APC – Ganduje  ‘Yan majalisar da aka dakatar sun hada da Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila, mai wakiltar Kano ta Kudu a majalisar dattawa, da kuma ‘yan majalisar wakilai uku, wato Alhaji Abdullahi Sani Rogo (Mazabar Tarayya ta Rogo), Alhaji Abdullahi Rurum (Mazabar Tarayya ta Rano/Kibiya), da Ali Madakin Gini (Mazabar Tarayya ta Dala). LEADERSHIP na zargin cewa, daya daga cikin al’amarin da ya jawo dakatarwar shi ne gayyatar da fitattun shugabannin jam’iyyar APC na kasa, da suka hada da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, suka yi a kwanakin baya, tare da tsohon Gwamna Ibrahim Shekarau, zuwa wani taro da Sanata Sumaila ya shirya. Tarukan sun hada da daurin auren diyarsa da bikin yaye dalibai na farko a jami’ar sa mai zaman kanta dake karamar hukumar Sumaila. Kasancewar shugabannin jam’iyyar APC a wajen taron, kuma an ki gayyatar ‘ya’yan jam’iyyar NNPP, ya janyo ce-ce-ku-ce a kan yiwuwar komawar Sumaila zuwa APC. Shugaban NNPP, ya kuma bayyana cewa jam’iyyar za ta kafa wani kwamiti da zai binciki lamarin tare da daukar matakin da ya dace da su a nan gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan majalisar majalisar da

এছাড়াও পড়ুন:

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Bayan hakan, Pogba ya kunce kwantiraginsa da Juventus a watan Nuwamban 2024, kuma tun watan Maris da ya gabata ya samu damar komawa fili domin shirya dawowarsa.

Yanzu haka yana ci gaba da atisaye tare da fatan ƙulla sabuwar yarjejeniya da Monaco domin ci gaba da taka leda a ƙasarsa ta haihuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Abokin Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje