Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn
Published: 22nd, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Yobe, ta rattaba hannu kan kwangilar gina gadar sama da titin ƙarƙashin ƙasa a tsakiyar garin Damaturu, Babban Birnin Jihar, kan kuɗi Naira biliyan 22.3.
Wannan wani mataki ne na ci gaba a ƙoƙarin gwamnatin samar wa al’umma ababen more rayuwa.
Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna AdelekeKwamishinan ayyuka na jihar, Injiniya Umar Duddaye ne, ya sanya hannu a madadin gwamnati, yayin da Injiniya Habib Geojea ya wakilci kamfanin da zai aiwatar da aikin, Messrs Triacta Nigeria Limited.
Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnatin Mai Mala Buni na bai wa manyan ayyukan ci gaba fifiko, wanda ya haɗa da tituna, gadoji, da magudanun ruwa.
Ya ce aikin gadar sama da ke shatale-shatalen Damaturu za a kammala shi cikin watanni 12.
Haka nan, an rattaba hannu kan kwangilar gina titin Damaturu zuwa Gambir tsakanin gwamnatin Yobe da kamfanin Messrs Elegance Construction Nigeria Limited, wanda za a kammala cikin watanni tara.
Kwamishinan ya ƙara da cewa ana shirin gina sabbin tituna masu tsawon kilomita 23.5 da magudanan ruwa masu nisan kilomita 27 a Damaturu, tare da sake da gyara titunan da ake buƙata.
Aikin zai shiga mataki na biyu a shekarar 2025.
Manajan yanki naTriacta Nigeria Limited ya tabbatar da cewa za su gudanar da aikin cikin inganci da wa’adin da aka tsara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gadar Sama
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.
Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.
A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp