Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke ya ce ya sha alwashin cewa zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi a jihar a gobe Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a matsayin martani kan shawarar da ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi, wanda ya buƙaci gwamnatin jihar ta dakatar da yunƙurin yin sabon zaɓen ƙananan hukumomi.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, Ministan ya ce kotu ta dawo da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da aka zaɓa a ƙarƙashin tsohon Gwamna Gboyega Oyetola, amma ta tsige su ta hanyar umarnin zartarwa da gwamnan ya yi.
Fagbemi ya ce ba bisa ƙa’ida ba ne a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Osun kafin watan Oktoba lokacin da wa’adin shugabanni da kansilolin da aka zaɓa a Jam’iyyar APC zai ƙare.
Sai dai a wata sanarwa da kakakin Gwamnan, Olawale Rasheed ya fitar, gwamnan ya ce mutanen jihar a shirye suke tsaf kuma babu gudu babu ja da baya kan gudanar da zaɓen.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karɓar rukunin gamayyar ƙungiyoyin farar hula da suka je jihar domin sanya ido kan zaɓen ƙananan hukumomi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnan Jihar Osun zaɓen ƙananan
এছাড়াও পড়ুন:
Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.
Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.
Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwaCikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.
Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).
’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.
Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.
Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.