Aminiya:
2025-07-31@17:30:53 GMT

Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke

Published: 21st, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke ya ce ya sha alwashin cewa zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi a jihar a gobe Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a matsayin martani kan shawarar da ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi, wanda ya buƙaci gwamnatin jihar ta dakatar da yunƙurin yin sabon zaɓen ƙananan hukumomi.

Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Peter Obi An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, Ministan ya ce kotu ta dawo da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da aka zaɓa a ƙarƙashin tsohon Gwamna Gboyega Oyetola, amma ta tsige su ta hanyar umarnin zartarwa da gwamnan ya yi.

Fagbemi ya ce ba bisa ƙa’ida ba ne a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Osun kafin watan Oktoba lokacin da wa’adin shugabanni da kansilolin da aka zaɓa a Jam’iyyar APC zai ƙare.

Sai dai a wata sanarwa da kakakin Gwamnan, Olawale Rasheed ya fitar, gwamnan ya ce mutanen jihar a shirye suke tsaf kuma babu gudu babu ja da baya kan gudanar da zaɓen.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karɓar rukunin gamayyar ƙungiyoyin farar hula da suka je jihar domin sanya ido kan zaɓen ƙananan hukumomi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Jihar Osun zaɓen ƙananan

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗa Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Gusau kuma Sarkin Katsina na Masarautar Gusau.

Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da hakan, inda ya bayyana cewa an yi naɗin ne bisa ga shawarwarin da masu zaɓen sarakuna na masarautar Gusau suka bayar, tare da bin al’ada da dokokin da suka dace.

A wata sanarwa da mai taimakawa na musamman kan harkokin yaɗa labarai a ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ya ce sabon Sarkin, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, shi ne ɗa na farko ga marigayi Sarki, kuma kafin naɗin nasa yana riƙe da mukamin Bunun Gusau.

Alhaji Abdulkadir ya hau karagar mulki a matsayin Sarkin Gusau na 16, bayan rasuwar mahaifinsa, Mai Martaba Dokta Ibrahim Bello, wanda ya rasu a ranar 25 ga Yulin 2025, bayan shafe shekara goma yana mulki.

Yayin da yake taya sabon sarkin murna, Gwamna Lawal ya bukace shi da ya ci gaba da rike kyakkyawar jagoranci da mutumtaka da aka san kakanninsa da shi, musamman kasancewarsa  tsatson Malam Sambo Dan Ashafa.

Gwamnan ya kuma bukaci sabon Sarkin da ya kasance jajirtacce wajen kawo haɗin kai, zaman lafiya da cigaba, tare da ƙarfafa hadin kai  a ciki da wajen masarautar Gusau.

 

Daga Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati