Aminiya:
2025-09-18@03:48:12 GMT

Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista

Published: 21st, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa ba ta shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje ba, duk da cewa farashin kayan abinci ya ragu a kasuwanni.

Ministan Aikin Gona da Samar da Abinci, Farfesa Abubakar Kyari, ya bayyana cewa, ko da yake gwamnatin ta yi tunanin shigo da abinci a lokacin da farashinsa ya yi tashin gwauron zabo, daga bisani ta janye wannan shawarar.

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu

Ministan ya danganta saukar farashin kayan abinci da ƙoƙarin manoma da suka koma gonaki a daminar bara, wanda ya sa amfanin gona ya yi yawa.

Ya kuma buƙaci ‘yan kasuwa da su rage farashi domin jama’a su samu sauƙin rayuwa.

Sai dai wasu rahotanni sun bayyana cewa saukar farashin kayan abincin na da alaƙa da wasu dalilai da suka haɗa da shigo da wasu nau’ikan kayan abinci daga waje ba tare da haraji ba.

Wannan mataki da gwamnati ta ɗauka ya taimaka wajen ƙara wadatuwar kayan abinci a kasuwanni, lamarin da ke hana farashinsu tashi.

Har ila yau, ana cikin lokacin girbi, wanda ya sa manoma da yawa suka fito da amfanin gonarsu zuwa kasuwanni.

Yawaitar kayan abinci a hannun ’yan kasuwa ya rage farashin kayayyaki kamar shinkafa, gero, dawa, da wake.

Wani babban dalili da masana tattalin arziƙi suka bayyana shi ne, farfaɗowar darajar Naira a kasuwar musayar kuɗi.

Saukar darajar dala ya sa kayan abinci da ake shigo da su daga waje sun yi sauƙi idan aka kwatanta da watannin baya.

Tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin rage tsadar rayuwa, ciki har da sauƙaƙa shigo da abinci, sun taka muhimmiyar rawa wajen rage hauhawar farashi a kasuwanni.

Wannan mataki na ci gaba da samar da sauƙi ga jama’a yayin da ake fatan farashin kayan abinci zai ci gaba da yin ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa Kayan abinci Masara Ministan Harkokin Noma farashin kayan abinci kayan abinci da a kasuwanni

এছাড়াও পড়ুন:

Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare

Fitattun dalibai akalla 12 ne  daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare  a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).

A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.

Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.

A cewarsa, an zabo daliban 12 ne  sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.

Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.

“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.

Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.

A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.

Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin