Aminiya:
2025-11-03@01:29:05 GMT

Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista

Published: 21st, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa ba ta shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje ba, duk da cewa farashin kayan abinci ya ragu a kasuwanni.

Ministan Aikin Gona da Samar da Abinci, Farfesa Abubakar Kyari, ya bayyana cewa, ko da yake gwamnatin ta yi tunanin shigo da abinci a lokacin da farashinsa ya yi tashin gwauron zabo, daga bisani ta janye wannan shawarar.

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu

Ministan ya danganta saukar farashin kayan abinci da ƙoƙarin manoma da suka koma gonaki a daminar bara, wanda ya sa amfanin gona ya yi yawa.

Ya kuma buƙaci ‘yan kasuwa da su rage farashi domin jama’a su samu sauƙin rayuwa.

Sai dai wasu rahotanni sun bayyana cewa saukar farashin kayan abincin na da alaƙa da wasu dalilai da suka haɗa da shigo da wasu nau’ikan kayan abinci daga waje ba tare da haraji ba.

Wannan mataki da gwamnati ta ɗauka ya taimaka wajen ƙara wadatuwar kayan abinci a kasuwanni, lamarin da ke hana farashinsu tashi.

Har ila yau, ana cikin lokacin girbi, wanda ya sa manoma da yawa suka fito da amfanin gonarsu zuwa kasuwanni.

Yawaitar kayan abinci a hannun ’yan kasuwa ya rage farashin kayayyaki kamar shinkafa, gero, dawa, da wake.

Wani babban dalili da masana tattalin arziƙi suka bayyana shi ne, farfaɗowar darajar Naira a kasuwar musayar kuɗi.

Saukar darajar dala ya sa kayan abinci da ake shigo da su daga waje sun yi sauƙi idan aka kwatanta da watannin baya.

Tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin rage tsadar rayuwa, ciki har da sauƙaƙa shigo da abinci, sun taka muhimmiyar rawa wajen rage hauhawar farashi a kasuwanni.

Wannan mataki na ci gaba da samar da sauƙi ga jama’a yayin da ake fatan farashin kayan abinci zai ci gaba da yin ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa Kayan abinci Masara Ministan Harkokin Noma farashin kayan abinci kayan abinci da a kasuwanni

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.

 

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025 Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP