Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Published: 21st, February 2025 GMT
Tarkon Dark Web: Wasu yara na iya fada cikin rukunin yanar gizo da ke da hadari.
Dabara Da Yaudara A Wasanni (Gaming Scams): Wasu yara na fuskantar barazana a cikin wasannin da suke bugawa online.
Yadda Za A Kare Yara Daga Wadannan Barazanar
Iyaye su lura da abin da yaran su ke yi online – Kula da shafukan da suke ziyarta da kuma mutanen da suke magana da su.
Amfani da ‘Parental Control’ – A saita wayoyin yara domin hana shiga shafuka masu illa.
Ilimantar da yara kan sirri – A koya musu kada su bada bayanan sirrinsu kamar lambar waya, adireshi, ko hotuna.
Kafa iyaka kan amfani da intanet – Iyaye su saka ka’ida kan lokacin da yara za su rika amfani da intanet.
Sanin abokansu na online – Iyaye su bincika su san wanda yaran su ke hulda da su a WhatsApp, Facebook, da sauran shafuka.
Guje wa kyauta ko aikawa da kudi online – A hana yara karbar ko aika wa da kudi ga mutane da ba su sani ba.
Kar a saka Hotuna masu fallasa – Iyaye su koyar da yara cewa duk abin da aka saka a intanet yana nan har abada.
Labari Mai karfafa Gwiwa
Akwai wani yaro mai suna Abdul, mai shekaru 12. Ya saba danna duk wani link da ya gani a Facebook. Wata rana, ya bude wani link wanda ya yi downloading na wani application da ba shi da lafiya. Wannan application ya dauke bayanansa kuma ya aika wa wani mutum wanda bai sani ba. Sai dai da yake iyayensa sun koya masa kada ya bayyana bayanansa, bai bayar da lambar katinsa ba, hakan yasa bai fada tarkon zamba ba. Wannan na nuna cewa idan iyaye suka koya wa yaran su yadda za su yi taka tsantsan, hakan na iya ceton su daga hatsarin intanet.
Kammalawa
Iyaye su fahimci cewa intanet yana da amfani, amma yana da hatsarori. Muna bukatar wayar da kan yara da matasa a kan yadda za su kare kansu. Ku kasance masu lura da irin shafukan da yaran ku ke ziyarta don kare su daga barazanar duniya ta yanar gizo.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
কীওয়ার্ড: Yara
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
Iran ta kai sabbin hare-hare kan manyan biranen Isra’ila da suka haɗa da Tel Aviv da Haifa, inda ta yi amfani da makaman linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa.
A cewar gidan talabijin na Iran, gomman makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa ne suka tashi zuwa Isra’ila, kuma wasu daga cikinsu sun ƙetare garkuwar kariyar iska ta Isra’ila.
An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensaSai dai har yanzu ba a ji wani bayani daga sojojin Isra’ila ba.
Faɗan Iran da Isra’ila ya fara ne bayan Isra’ila ta kai hari kan wani sashen ofishin jakadancin Iran da ke birnin Damascus na Siriya, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu manyan jami’an Iran.
Wannan mataki ya tayar da hankalin Iran, inda ta sha alwashin ramawa kuma wannan hari da ta kai yanzu na daga cikin mayar da martani kan harin Isra’ila.