Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Published: 21st, February 2025 GMT
Tarkon Dark Web: Wasu yara na iya fada cikin rukunin yanar gizo da ke da hadari.
Dabara Da Yaudara A Wasanni (Gaming Scams): Wasu yara na fuskantar barazana a cikin wasannin da suke bugawa online.
Yadda Za A Kare Yara Daga Wadannan Barazanar
Iyaye su lura da abin da yaran su ke yi online – Kula da shafukan da suke ziyarta da kuma mutanen da suke magana da su.
Amfani da ‘Parental Control’ – A saita wayoyin yara domin hana shiga shafuka masu illa.
Ilimantar da yara kan sirri – A koya musu kada su bada bayanan sirrinsu kamar lambar waya, adireshi, ko hotuna.
Kafa iyaka kan amfani da intanet – Iyaye su saka ka’ida kan lokacin da yara za su rika amfani da intanet.
Sanin abokansu na online – Iyaye su bincika su san wanda yaran su ke hulda da su a WhatsApp, Facebook, da sauran shafuka.
Guje wa kyauta ko aikawa da kudi online – A hana yara karbar ko aika wa da kudi ga mutane da ba su sani ba.
Kar a saka Hotuna masu fallasa – Iyaye su koyar da yara cewa duk abin da aka saka a intanet yana nan har abada.
Labari Mai karfafa Gwiwa
Akwai wani yaro mai suna Abdul, mai shekaru 12. Ya saba danna duk wani link da ya gani a Facebook. Wata rana, ya bude wani link wanda ya yi downloading na wani application da ba shi da lafiya. Wannan application ya dauke bayanansa kuma ya aika wa wani mutum wanda bai sani ba. Sai dai da yake iyayensa sun koya masa kada ya bayyana bayanansa, bai bayar da lambar katinsa ba, hakan yasa bai fada tarkon zamba ba. Wannan na nuna cewa idan iyaye suka koya wa yaran su yadda za su yi taka tsantsan, hakan na iya ceton su daga hatsarin intanet.
Kammalawa
Iyaye su fahimci cewa intanet yana da amfani, amma yana da hatsarori. Muna bukatar wayar da kan yara da matasa a kan yadda za su kare kansu. Ku kasance masu lura da irin shafukan da yaran ku ke ziyarta don kare su daga barazanar duniya ta yanar gizo.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
কীওয়ার্ড: Yara
এছাড়াও পড়ুন:
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Duk da cewa suna da karfi a fannin aikin soja, amma harinsu zai zama tamkar amfani da igwa ne wajen kashe sauro. Duk wani fifikon da suke da shi ba zai dore ba. Saboda haka, a zahiri wannan tambayar da wani mai amfani da yanar gizo ya yi, ta nuna rashin hankali cikin kalaman shugaban Amurka.
Sai dai kalaman sun dace da halayya, da salon musamman na shugaba Donald Trump. Wani lokaci, da gangan ya kan yi amfani da kalmomi, da aikace-aikace marasa ma’ana wajen samar da yanayi na rashin tabbas, ta yadda zai samu damar matsawa wani lamba, don tilasta masa ya yi wani aiki. Wannan dabara ce da wasu masanan kasar Amurka ke kira da “ka’idar mahaukaci”, watakila ta dace da halayyar shugaba Trump, abun da ya sa yake ta amfani da ita wajen kula da harkokin waje.
Kana wannan batu na yin barazanar kai hari ya dace da halayyar kasar Amurka. Kasa ce wadda ba ta mai da hankali a kan neman gano gaskiya ba, balle ma la’akari da bayanan da Nijeriya ta gabatar dangane da zargin da aka yi mata. Kai tsaye an yi fatali da ikon mulkin kai na Najeriya, da dokokin kasa da kasa, da ra’ayoyin kasashen yankin da ake ciki. A ganin kasar Amurka, tana iya tsoma baki a duk wani aiki, da aikata yadda ta ga dama, kuma idan za ta iya yin amfani da karfin tuwo wajen tilasta wani, to ba za ta taba tattaunawa da shi ba. Kawai kasar tana kokarin aiwatar da mulkin danniya ne a duniya.
Amma, a cewar wasu masana, “ka’idar mahaukaci” ba ko yaushe take yin tasiri ba. Saboda idan wani ya dade yana kwaikwayon mahaukaci, to, ba za a ci gaba da tsoronsa ba. Kana mulkin danniya na kasar Amurka shi ma ba zai dore ba, idan aka yi la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke tasowa cikin sauri a zamanin da muke ciki.
Ko ta yaya ya kamata Amurka ta daidaita kalamanta da ayyukanta? Kuma ta wace hanya ya kamata kasashe daban daban su yi mu’ammala da juna?
Na farko, ya kamata mu tabbatar da daidaito tsakanin mabambanta kasashe, da kuma bin dokokin kasa da kasa. Na biyu, ya kamata mu daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da neman daidaita harkoki ta hanyar yin shawarwari, maimakon tayar da rikici. Na uku, ya kamata mu dora muhimmanci kan jin dadin jama’a, ta yadda ba za a tsaya ga kula da mutanen gida kadai ba, wato a hada da al’ummun sauran kasashe. Ya kamata a lura da hakkinsu da bukatunsu. Wadannan abubuwa suna cikin shawarar da kasar Sin ta gabatar, dangane da inganta jagorancin duniya.
Watakila kasar Amurka ba ta yarda da wadannan ka’idoji ba tukuna, amma tabbas wata rana za ta amince da su. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA