Leadership News Hausa:
2025-07-31@20:10:21 GMT

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

Published: 21st, February 2025 GMT

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

 

Tarkon Dark Web: Wasu yara na iya fada cikin rukunin yanar gizo da ke da hadari.

 

Dabara Da Yaudara A Wasanni (Gaming Scams): Wasu yara na fuskantar barazana a cikin wasannin da suke bugawa online.

Yadda Za A Kare Yara Daga Wadannan Barazanar

Iyaye su lura da abin da yaran su ke yi online – Kula da shafukan da suke ziyarta da kuma mutanen da suke magana da su.

Amfani da ‘Parental Control’ – A saita wayoyin yara domin hana shiga shafuka masu illa.

Ilimantar da yara kan sirri – A koya musu kada su bada bayanan sirrinsu kamar lambar waya, adireshi, ko hotuna.

Kafa iyaka kan amfani da intanet – Iyaye su saka ka’ida kan lokacin da yara za su rika amfani da intanet.

Sanin abokansu na online – Iyaye su bincika su san wanda yaran su ke hulda da su a WhatsApp, Facebook, da sauran shafuka.

Guje wa kyauta ko aikawa da kudi online – A hana yara karbar ko aika wa da kudi ga mutane da ba su sani ba.

Kar a saka Hotuna masu fallasa – Iyaye su koyar da yara cewa duk abin da aka saka a intanet yana nan har abada.

 

Labari Mai karfafa Gwiwa

Akwai wani yaro mai suna Abdul, mai shekaru 12. Ya saba danna duk wani link da ya gani a Facebook. Wata rana, ya bude wani link wanda ya yi downloading na wani application da ba shi da lafiya. Wannan application ya dauke bayanansa kuma ya aika wa wani mutum wanda bai sani ba. Sai dai da yake iyayensa sun koya masa kada ya bayyana bayanansa, bai bayar da lambar katinsa ba, hakan yasa bai fada tarkon zamba ba. Wannan na nuna cewa idan iyaye suka koya wa yaran su yadda za su yi taka tsantsan, hakan na iya ceton su daga hatsarin intanet.

 

Kammalawa

Iyaye su fahimci cewa intanet yana da amfani, amma yana da hatsarori. Muna bukatar wayar da kan yara da matasa a kan yadda za su kare kansu. Ku kasance masu lura da irin shafukan da yaran ku ke ziyarta don kare su daga barazanar duniya ta yanar gizo.

Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yara

এছাড়াও পড়ুন:

Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 

Wani mutum ya rasu yayin da yake ƙoƙarin raba wani mutum da matarsa da fada a yankin Babban Birnin Tarayya.

Da farko mutumin ya faɗi ne a sume kafin daga bisani rai ya yi halinsa a yankin Dogon-Ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Abaji.

Wani ganau, Barnabas Yakubu, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da yamma ne ma’auratan, waɗanda makwabta ne ga mamacin, suka fara faɗa ne bayan wata rashin fahimta, shi kuma Ayuba, bayan jin hayaniyar, ya fito daga ɗakinsa don shiga tsakani.

A cewarsa, mamacin ya dawo ne daga gonarsa kuma yana shirin yin wanka lokacin da ya ji maƙwabcinsa yana dukan matarsa.

Ya ce, Ayuba nan take ya ajiye soso da gugar ruwansa ya ruga don shiga tsakani amma ya faɗi sumamme a yayin.

Ayuba, wanda aka yi imanin yana cikin koshin lafiya kafin faruwar lamarin, an garzaya da shi asibiti a garin Gawu, inda likitocin da ke bakin aiki suka tabbatar da mutuwarsa.

Sarkin yankin, bayan samun labarin lamarin, ya sanar da ’yan banga tare da ba da umarnin kama ma’auratan, waɗanda daga baya aka mika su ga jami’an tsaro a Gawu.

Ibrahim, daya daga cikin ’yan bangan, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa, “Mun fahimci cewa ƙaramar rashin fahimta ce kawai ta kai ga faɗan tsakanin makwabcin mamacin da matarsa.”

Ya ƙara da cewa an kai gawar mamacin kauyensa na Paiko a Jihar Neja don binnewa.

’Yan sanda a yankin Gawu sun tabbatar da faruwar lamarin, inda suka ce har yanzu ana ci gaba da bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata