Aminiya:
2025-07-31@16:41:35 GMT

An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB

Published: 21st, February 2025 GMT

Hamshakan attajirai da ’yan siyasa sun bayar da gudunmawar sama da Naira biliyan 16 a bikin kaddamar da littafin tarihin tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida.

Taron ƙaddamar da littafin, mai suna ‘A Journey in Service’, wanda aka gudanar a Abuja ya tara manyan baƙi daga ciki da wajen Najeriya.

Mahalarta taron da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis sun bayar da gudunmawar ne domin ginin dakin karatun da tsohon shugaban ƙasan ke shirin ginawa. Attajiri mafi yawan arziki a Afirka kuma Shugaban Rukunin Kamfanonin Ɗangote, Alhaji Alikon Ɗangote ya ba da gudunmawar Naira biliyan takwas, Naira biliyan biyu a duk shekara, na tsawon shekara huɗu. Ya kuma yi alƙawarin karin biliyan biyu a duk shekara har a gama aikin. NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida

A nasa ɓangaren, Shugaban Rukunin Kamfanonin BUA, ya ba da gudunmawar Naira biliyan biyar.

Tsohon Ministan Taro kuma Shugaban Gidauniyar TY, Janar Theophelus Ɗanjuma, ya bayar da Naira biliyan uku.

Babban attajiri a yankin Kudu, Arthur Eze, ya ba da Naira miliyan 500.

Sanata Sani Musa ya ba da miliyan N250 a yayin da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ba da miliyan N50.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Barau Jibrin ya ba da Naira miliyan 20 a yayin da Sanata Aliyu Wadada ya ba da miliyan 10.

Hamshakiyar ’yan kasuwa Folorunsho Alakija, da wasu fitattun ’yan Najeriya sun bayyana gudunmawa, amma ba su sanarna bainar jama’a ba.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci tsoffin shugaban kasa na farar hula na mulkin soji irinsu Goodluck Jonathan, Yakubu Gowon, Abdulsalami Abubakar, da wasu manyan baƙi.

Tsoffin mataimakan shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar da Muhammad Namadi Sambo da Yemi Osinbajo.

Hakazalika dan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da takwaransa na Jam’iyyar LP, Peter Obi, sun samu halartar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Naira biliyan da gudunmawar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22

An shawarci gwamnatocin jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara da su kirkiro hanyoyi na wayar da kan al’umma dangane da shirye-shiryen tallafi da ayyukan ci gaba da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa domin bunkasa tattalin arziki da tabbatar da tsaro a yankunansu.

Shugaban sashen kimiyyar zamantakewa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Chika Umar Aliyu, ne ya bayar da wannan shawara yayin gabatar da takarda a wajen taron shekara-shekara na kungiyar Nigerian Institute of Management reshen jihar Sokoto na shekarar 2025, wanda aka hada da gabatar da lambar yabo ga wadanda suka cancanta.

 

Farfesa Chika ya bayyana cewa, gwamnati tarayya na da shirye-shiryen tallafi da dama da suka hada da na noma, kasuwanci da kuma koyar da sana’o’in hannu domin kara habaka tattalin arzikin ‘yan Najeriya da rage zaman kashe wando, da tayar da hankali musamman matasa a yankin.

Ya jaddada cewa dole ne gwamnatocin jihohi su tallafa wa kokarin gwamnatin tarayya ta hanyar amfani da hukumominsu na jin dadin al’umma domin cimma burin shirye-shiryen.

A jawabinsa wajen taron, kwamishinan noma na jihar Sakkwato, Muhammad Tukur Alkali, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta sayo manyan Tan-tan na noma guda 250 da kayan aikin gona da darajarsu ta kai naira biliyan ashirin da biyu da miliyan dari daya (₦22.1bn), domin tabbatar da wadatar abinci.

A cewar Tukur Alkali, gwamnatin jihar ta hanyar shirye-shiryen inganta rayuwar al’umma, ta samar da sama da ayyukan yi 2,700 a bangaren noma, abin da ke da tasiri mai girma wajen bunkasa noma mai dorewa da ci gaban ababen more rayuwa a karkara.

Daga Nasir Malali

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata