Gwamnati Za Ta Haramta Amfani Da Tankoki Masu Ɗaukar Lita 60,000 Aiki Daga Maris 1.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da zagayen farko na makon lafiyar mata da jarirai da jarirai (MNCHW) na shekarar 2025 tare da raba fakiti 6,000 na kayan haihuwa da na’urar (C/S) 500 ga cibiyoyin lafiya a fadin jihar.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta shi ne ya jagoranci bikin kaddamar da shirin a hukumance da aka gudanar a cibiyar lafiya matakin farko na Birji da ke karamar hukumar Madobi.

 

Ya yi nuni da cewa, wannan aikin ya hada da na rigakafi na yau da kullun ga yara, karin sinadarin Vitamin A, Rarraba gidajen sauro masu maganin kwari ga mata masu juna biyu.

 

Gwamna Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na karfafa wa shirin rabon gidajen sauro ta hanyar ware naira miliyan 140 domin adana gidajen sauro da aka raba.

 

Gwamnan ya bukaci mata da masu kulawa da su yi amfani da damar da za a yi na tsawon mako guda don samun muhimman ayyukan kiwon lafiya da ake bayarwa kyauta.

 

A cikin sakon sa na fatan alheri, shugabar ofishin UNICEF a Kano, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta kara yawan kwanakin hutun haihuwa da ake biyarwa domin kare lafiyar mata da jarirai da kuma inganta shayar da jarirai nonon uwa zalla.

 

Taron ya samu halartar kwamishinan lafiya, shugaban karamar hukumar Madobi, Hakimin Shanono, abokan cigaba, masu rike da mukaman siyasa da duk masu ruwa da tsaki.

 

 

COV/Khadija Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza
  • Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya