Aminiya:
2025-06-15@08:21:03 GMT

Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump

Published: 19th, February 2025 GMT

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya soki shugabancin Ukraine, inda ya bayyana cewar su ne suka haddasa yaƙin da Rasha ke yi da su.

Trump, ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, wanda ya ce yana mamakin yadda ba a gayyaci ƙasarsa zuwa taron tattaunawar zaman lafiya a Saudiyya ba.

’Yan bindiga sun kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa

A cewar Trump, Ukraine ce ta jawo wa kanta matsalar.

“Da ba ku fara wannan yaƙin ba, da kun cimma yarjejeniya tun farko,” in ji shi.

“Da ni ne, da na samo muku mafita, kuma babu wanda za a kashe.”

A Saudiyya, Rasha da Amurka sun fara tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin.

Ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya ce: “Ba za mu amince da dakarun Nato a Ukraine ba.”

Lavrov ya ce Rasha na son tattaunawa, amma ba za ta yarda da wata yarjejeniya da za ta bai wa Nato damar girke dakarunta a Ukraine ba.

A nasa ɓangaren, Zelensky ya mayar da martani da cewa Rasha ba abin dogaro ba ce.

“Rasha ba abin yarda ba ce. Dole ne a tilasta mata zaman lafiya.”

Trump ya kuma soki Ukraine kan rashin gudanar da zaɓe tun bayan fara yaƙin.

“Shin ’yan Ukraine ba za su iya fita su zaɓi shugabansu ba? An ɗauki tsawon lokaci ba a yi zaɓe ba.”

Ya ƙara da cewa Ukraine ta rasa goyon bayan jama’arta, yana mai iƙirarin cewa Zelensky ya rasa kashi huɗu cikin 10 na magoya bayansa.

A yayin da ake ci gaba da rikici, Amurka da ƙasashen Turai na ƙoƙarin samun mafita, amma Trump ya ce Amurka ba za ta tura dakarunta zuwa Ukraine ba.

“Idan Turawa suna son yin yaƙi, abu ne mai kyau, ina goyon baya,” in ji Trump.

“Amma Amurka ba ta da nasaba da wannan rikici.”

Taron Saudiyya dai na ɗaya daga cikin matakan tattaunawa tsakanin manyan ƙasashen don kawo ƙarshen wannan rikici, wanda ya haddasa asarar rayuka tun a shekarar 2022.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya tattaunawa Ukraine yaƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa

Yayin da damina ke ƙara ƙaratowa, Gwamnatin Jihar Kano, ta fara wani aikin tsaftace manyan magudanan ruwa domin daƙile aukuwar ambaliyar ruwa.

An fara aikin ne a yankin shataletalen Baban Gwari, ɗaya daga cikin wuraren da ambaliya ke yawan aukuwa a Birnin Kano.

Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ce ke jagorantar aikin tsaftace magudanan ruwan.

Wannan mataki na daga cikin shirin gwamnatin jihar na kare rayuka, dukiyoyi, da kuma inganta ababen more rayuwa.

A lokacin ƙaddamar da aikin, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Hashim Muhammad Dahiru, ya bayyana cewa an zaɓi Baban Gwari saboda muhimmancinsa da kuma yadda wajen yake a lokacin damina.

Ya ce wajen ya daɗe da zama wajen zubar da shara barkatai da kuma toshe hanyoyin ruwa.

Ya ƙara da cewa wannan wajen ba wai kawai muhimmiyar mahaɗa ba ce, amma kuma yana ɗaya daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ke da alaƙa da ruwan Jakara da Kwarin Gogau.

Kwamishinan ya bayyana cewa mazauna yankin da masu wucewa sun sha fuskantar ambaliya da ta shafi rayuwarsu, lafiyarsu da kuma zirga-zirgarsu.

Ya ce wannan aikin ba na al’ada ba ce, illa alama ce da ke nuna cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin kare muhalli da kuma samar da birni mai jure sauyin yanayi da ambaliya.

Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jagoranci da goyon bayan da ya bai wa ma’aikatar wajen aiwatar da wannan aiki.

Ya ce gwamnatin ta amince da sanya tsaftace magudanan ruwa a matsayin aikin da za a riƙa gudanarwa a kowace shekara domin tabbatar da tsaftar hanyoyin ruwa a faɗin jihar.

Haka kuma, gwamnatin ta bayar da kwangilar gyaran shataletalen Baban Gwari domin inganta zirga-zirga da rage yawan ambaliya, ta hanyar gina sabbin hanyoyin ruwa.

Kwamishinan ya bayyana cewa waɗannan matakai suna nuna irin hangen nesa da damuwar gwamnan jihar kan lafiyar jama’a da kuma kare su daga illolin da ke zuwa da ambaliya da sauyin yanayi.

Ya buƙaci jama’a da su daina zubar da shara barkatai, musamman a cikin magudanan ruwa, ya kuma buƙaci su riƙa ɗaukar nauyin tsaftace muhallinsu.

Ya ce gwamnatin za ta yi nata aikin, amma ana buƙatar haɗin gwiwar kowa da kowa domin a cimma nasara.

Ya kuma buƙaci ma’aikata da abokan aikin muhalli da su gudanar da aikinsu da kulawa da gaskiya, yana mai cewa aikin ba wai tsaftace magudanan ruwa ba ne kawai, amma aikin ne na kare rayuka, daƙile haɗura da kuma gina sabuwar Kano mai tsafta da lafiya.

A ’yan shekarun nan, yankin Baban Gwari ya yi ƙaurin suna wajen yawan aukuwar ambaliya, har ma da rasa rayuka da dukiyoyi.

Wannan ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa domin magance matsalar kafin saukar daminar bana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini