Aminiya:
2025-05-01@04:15:07 GMT

Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump

Published: 19th, February 2025 GMT

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya soki shugabancin Ukraine, inda ya bayyana cewar su ne suka haddasa yaƙin da Rasha ke yi da su.

Trump, ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, wanda ya ce yana mamakin yadda ba a gayyaci ƙasarsa zuwa taron tattaunawar zaman lafiya a Saudiyya ba.

’Yan bindiga sun kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa

A cewar Trump, Ukraine ce ta jawo wa kanta matsalar.

“Da ba ku fara wannan yaƙin ba, da kun cimma yarjejeniya tun farko,” in ji shi.

“Da ni ne, da na samo muku mafita, kuma babu wanda za a kashe.”

A Saudiyya, Rasha da Amurka sun fara tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin.

Ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya ce: “Ba za mu amince da dakarun Nato a Ukraine ba.”

Lavrov ya ce Rasha na son tattaunawa, amma ba za ta yarda da wata yarjejeniya da za ta bai wa Nato damar girke dakarunta a Ukraine ba.

A nasa ɓangaren, Zelensky ya mayar da martani da cewa Rasha ba abin dogaro ba ce.

“Rasha ba abin yarda ba ce. Dole ne a tilasta mata zaman lafiya.”

Trump ya kuma soki Ukraine kan rashin gudanar da zaɓe tun bayan fara yaƙin.

“Shin ’yan Ukraine ba za su iya fita su zaɓi shugabansu ba? An ɗauki tsawon lokaci ba a yi zaɓe ba.”

Ya ƙara da cewa Ukraine ta rasa goyon bayan jama’arta, yana mai iƙirarin cewa Zelensky ya rasa kashi huɗu cikin 10 na magoya bayansa.

A yayin da ake ci gaba da rikici, Amurka da ƙasashen Turai na ƙoƙarin samun mafita, amma Trump ya ce Amurka ba za ta tura dakarunta zuwa Ukraine ba.

“Idan Turawa suna son yin yaƙi, abu ne mai kyau, ina goyon baya,” in ji Trump.

“Amma Amurka ba ta da nasaba da wannan rikici.”

Taron Saudiyya dai na ɗaya daga cikin matakan tattaunawa tsakanin manyan ƙasashen don kawo ƙarshen wannan rikici, wanda ya haddasa asarar rayuka tun a shekarar 2022.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya tattaunawa Ukraine yaƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?

Wannan ya sa wasan yau zai zama mai ɗaukar hankali, domin kowanne daga cikinsu na burin ɗaukar kofin a karo na farko, domin a dakatar da yawan dariyar da ‘yan adawa ke musu.

A zagayen rukuni da suka haɗu a farkon wannan kakar, Arsenal ta lallasa PSG da ci 2-0.

Kocin Arsenal yanzu, Mikel Arteta, ya taɓa buga wasa a duka ƙungiyoyin.

Yana fatan ya zama kocin farko da zai jagoranci Arsenal ta lashe kofin Zakarun Turai.

Wannan ya sa magoya bayan Arsenal ke fatan ganin ƙungiyarsu ta yi abin mamaki a wasan da za a fara da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114