Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump
Published: 19th, February 2025 GMT
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya soki shugabancin Ukraine, inda ya bayyana cewar su ne suka haddasa yaƙin da Rasha ke yi da su.
Trump, ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, wanda ya ce yana mamakin yadda ba a gayyaci ƙasarsa zuwa taron tattaunawar zaman lafiya a Saudiyya ba.
A cewar Trump, Ukraine ce ta jawo wa kanta matsalar.
“Da ba ku fara wannan yaƙin ba, da kun cimma yarjejeniya tun farko,” in ji shi.
“Da ni ne, da na samo muku mafita, kuma babu wanda za a kashe.”
A Saudiyya, Rasha da Amurka sun fara tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin.
Ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya ce: “Ba za mu amince da dakarun Nato a Ukraine ba.”
Lavrov ya ce Rasha na son tattaunawa, amma ba za ta yarda da wata yarjejeniya da za ta bai wa Nato damar girke dakarunta a Ukraine ba.
A nasa ɓangaren, Zelensky ya mayar da martani da cewa Rasha ba abin dogaro ba ce.
“Rasha ba abin yarda ba ce. Dole ne a tilasta mata zaman lafiya.”
Trump ya kuma soki Ukraine kan rashin gudanar da zaɓe tun bayan fara yaƙin.
“Shin ’yan Ukraine ba za su iya fita su zaɓi shugabansu ba? An ɗauki tsawon lokaci ba a yi zaɓe ba.”
Ya ƙara da cewa Ukraine ta rasa goyon bayan jama’arta, yana mai iƙirarin cewa Zelensky ya rasa kashi huɗu cikin 10 na magoya bayansa.
A yayin da ake ci gaba da rikici, Amurka da ƙasashen Turai na ƙoƙarin samun mafita, amma Trump ya ce Amurka ba za ta tura dakarunta zuwa Ukraine ba.
“Idan Turawa suna son yin yaƙi, abu ne mai kyau, ina goyon baya,” in ji Trump.
“Amma Amurka ba ta da nasaba da wannan rikici.”
Taron Saudiyya dai na ɗaya daga cikin matakan tattaunawa tsakanin manyan ƙasashen don kawo ƙarshen wannan rikici, wanda ya haddasa asarar rayuka tun a shekarar 2022.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya tattaunawa Ukraine yaƙi
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.
Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura IsaTrump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”
A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.
“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”
Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.
“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.
Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.