Aminiya:
2025-04-30@23:16:47 GMT

Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara

Published: 19th, February 2025 GMT

Wani sabon rikici ya sake kunno kai a tsakanin manyan jam’iyyun siyasa biyu a Jihar Zamfara.

Rigimar wadda ta kunno tsakanin APC da PDP ta samo asali ne tun bayan da wasu matasa suka yi yunƙurin hana wani taro na ɗan Majalisar Wakilai da za a gudanar a garin Maru.

Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno

Hakan ya sa Gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta ɗauki wani matakin da take ganin zai kawo lafawar lamarin.

Sai dai kuma matakin da gwamnatin ta ɗauka bai yi wa jam’iyyar APC daɗi ba, inda ta nuna rashin gamsuwa tare da zargin ba a yi mata adalci ba saboda kasancewarta jam’iyyar adawa.

A bayan nan ne Gwamnatin Zamfara ta dakatar da duk wasu tarukan siyasa a jihar saboda samar da zaman lafiya da daidaito.

A bayanin da mai taimaka wa Gwamnan Zamfara kan kafafen yaɗa labarai, Mustapha Jafaru Kaura ya fitar, ya ce matakin na zuwa ne bayan hatsaniyar da aka samu a tsakanin jam’iyyun PDP da APC a Ƙaramar Hukumar Maru.

“Duk wani taron siyasa da zagaye an dakatar da shi a wannan lokaci, la’akari da abin da ya faru a Maru inda aka samu salwantar rayuka da ƙone-ƙonen dukiya.”

Hadimin gwamnan ya ce an ɗauki matakin ne ba don a musguna wa wasu ba face sai don samar da zaman lafiya kuma dokar da aka sanya ta wucin gadi ce.

Jam’iyyar APC a Zamfara ta nuna rashin gamsuwar ta kan matsayar da gwamnatin ta ɗauka tana mai zargin cewa gwamnatin ta mayar da hankali kan abin da ba shi ne ya fi ba.

Wata sanarwa da APC ta fitar ta bayyana cewa dole ne hukumar ’yan sanda a jiha ta kama waɗanda suka kai farmaki ga magoya bayanta a yayin da suke gudanar da kowane taro.

Jam’iyyar ta ce gargaɗin ya zama wajibi ganin yadda ‘yan sanda suka fita batun koken da aka gabatar musu a rubuce har guda uku.

“A cikin matasan da muke zargi, ’yan bangar siyasa daga jam’iyyar PDP da ’yan sa kai ne suka kawo farmaki a wurin rabon kayan ɗan Majalisar Wakilai na Maru da Bungudu, Honarabul Abdulmalik Zubairu Bungudu.

“Ɓatagarin sun laɓe ne kan hanyar Gusau zuwa Bungudu inda suka kai harin kan magoya bayan APC sannan suka lalata ababe hawa da dama.

Sakataren yaɗa labarai na APC a Zamfara, Yusuf Idris Gusau ya yi tir da lamarin, yana mai kiran jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

Idris Gusau ya ce “muddin ba haka ba zai sa mu riƙa kare kansu kan kowane mutum da ya nemi cin zarafinsu.”

Sakataren ya nemi magoya bayansu da su kwantar da hankali domin za a tabbatar da an yi adalci ga waɗanda aka ji wa rauni ko aka ɓarnata dukiyoyinsu.

“A matsayinmu na masu son zaman lafiyar Jihar Zamfara ba za mu bari a yi amfani da mu don kawo hargitsi ba kamar yadda jam’iyyar PDP ke kitsawa,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 

Ministan ya ce sabon gidan yanar na intanet zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da suka daɗe suna dagula harkokin sayayya a gwamnati, kamar yadda ake fama da rashin ingantattun tsare-tsare, ƙarancin ƙwararru da rashin tsarin horaswa na dindindin.

 

Ya ce: “Ƙaddamar da wannan sabon shafin ba kawai cigaba ba ne a fannin fasaha; wata babbar hanya ce ta sauya fasalin aiki gaba ɗaya wadda ke magance manyan ƙalubale a tsarin sayen kaya na gwamnati, irin su cikas da ke yawan faruwa, rashin ingantattun hanyoyin sayayya, ƙarancin ma’aikatan da suka dace, da kuma rashin ingantaccen tsarin gina ƙwarewa.

 

“Waɗannan matsaloli sun daɗe suna hana a yi amfani da dukiyoyin gwamnati yadda ya kamata tare da kawo cikas ga cigaban tattalin arziki gaba ɗaya a ƙasar nan.”

 

Ya ce wannan sabon tsari zai bai wa jami’an sayayya damar samun horo, takardun shaida, da kuma damar yin aiki da ƙwarewa, daidai da matakin duniya.

 

Idris ya ce: “Za a tabbatar da cewa mu jami’an gwamnati muna sayen kaya ba kawai bisa doka ba, har ma ƙwararru ne kuma masu iya gogayya a matakin duniya.”

 

Idris ya yaba wa Darakta-Janar na BPP, Dakta Adebowale Adedokun, bisa jajircewa da hangen nesan sa wajen inganta tsarin sayayya a Nijeriya.

 

Ya ce wannan gidan yana hujja ce ta jajircewar sa wajen ganin an sabunta tsarin sayayya a ƙasar nan.

 

Ministan ya kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su fahimci cewa sabon gidan yanar ba kawai don gwamnati ba ne, har ma wata hanya ce da za su iya amfani da ita wajen neman ingantattun ayyuka da gaskiya.

 

“Don haka ina kira ga dukkan hukumomi da jami’an gwamnati da su rungumi wannan shiri gaba ɗaya, kuma ina kira ga kafafen yaɗa labarai, musamman, da su taimaka wajen yaɗa amfanin sa da kuma sa ido kan yadda ake aiwatar da shi,” inji shi.

 

Cikin waɗanda suka halarci taron akwai Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Misis Didi Esther Walson-Jack; Ministan Kuɗi kuma Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Mista Wale Edun; Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa; Ministar Harkokin Mata, Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim; Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa (rtd); da Darakta-Janar na FRCN da NTA, Dakta Mohammed Bulama da Kwamared Abdulhamid Dembos.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara