Aminiya:
2025-08-01@01:16:49 GMT

Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara

Published: 19th, February 2025 GMT

Wani sabon rikici ya sake kunno kai a tsakanin manyan jam’iyyun siyasa biyu a Jihar Zamfara.

Rigimar wadda ta kunno tsakanin APC da PDP ta samo asali ne tun bayan da wasu matasa suka yi yunƙurin hana wani taro na ɗan Majalisar Wakilai da za a gudanar a garin Maru.

Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno

Hakan ya sa Gwamnatin Zamfara ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal ta ɗauki wani matakin da take ganin zai kawo lafawar lamarin.

Sai dai kuma matakin da gwamnatin ta ɗauka bai yi wa jam’iyyar APC daɗi ba, inda ta nuna rashin gamsuwa tare da zargin ba a yi mata adalci ba saboda kasancewarta jam’iyyar adawa.

A bayan nan ne Gwamnatin Zamfara ta dakatar da duk wasu tarukan siyasa a jihar saboda samar da zaman lafiya da daidaito.

A bayanin da mai taimaka wa Gwamnan Zamfara kan kafafen yaɗa labarai, Mustapha Jafaru Kaura ya fitar, ya ce matakin na zuwa ne bayan hatsaniyar da aka samu a tsakanin jam’iyyun PDP da APC a Ƙaramar Hukumar Maru.

“Duk wani taron siyasa da zagaye an dakatar da shi a wannan lokaci, la’akari da abin da ya faru a Maru inda aka samu salwantar rayuka da ƙone-ƙonen dukiya.”

Hadimin gwamnan ya ce an ɗauki matakin ne ba don a musguna wa wasu ba face sai don samar da zaman lafiya kuma dokar da aka sanya ta wucin gadi ce.

Jam’iyyar APC a Zamfara ta nuna rashin gamsuwar ta kan matsayar da gwamnatin ta ɗauka tana mai zargin cewa gwamnatin ta mayar da hankali kan abin da ba shi ne ya fi ba.

Wata sanarwa da APC ta fitar ta bayyana cewa dole ne hukumar ’yan sanda a jiha ta kama waɗanda suka kai farmaki ga magoya bayanta a yayin da suke gudanar da kowane taro.

Jam’iyyar ta ce gargaɗin ya zama wajibi ganin yadda ‘yan sanda suka fita batun koken da aka gabatar musu a rubuce har guda uku.

“A cikin matasan da muke zargi, ’yan bangar siyasa daga jam’iyyar PDP da ’yan sa kai ne suka kawo farmaki a wurin rabon kayan ɗan Majalisar Wakilai na Maru da Bungudu, Honarabul Abdulmalik Zubairu Bungudu.

“Ɓatagarin sun laɓe ne kan hanyar Gusau zuwa Bungudu inda suka kai harin kan magoya bayan APC sannan suka lalata ababe hawa da dama.

Sakataren yaɗa labarai na APC a Zamfara, Yusuf Idris Gusau ya yi tir da lamarin, yana mai kiran jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

Idris Gusau ya ce “muddin ba haka ba zai sa mu riƙa kare kansu kan kowane mutum da ya nemi cin zarafinsu.”

Sakataren ya nemi magoya bayansu da su kwantar da hankali domin za a tabbatar da an yi adalci ga waɗanda aka ji wa rauni ko aka ɓarnata dukiyoyinsu.

“A matsayinmu na masu son zaman lafiyar Jihar Zamfara ba za mu bari a yi amfani da mu don kawo hargitsi ba kamar yadda jam’iyyar PDP ke kitsawa,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana

Ɗaya daga cikin jigo da suka kafa Jam’iyyar PDP, Farfesa Jerry Gana ya yi iƙirarin cewa tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi zai kayar da duk wani ɗan takara a jihohin Arewacin Najeriya idan ya tsaya takara a PDP.

Da yake bayabni a tashar talabijin ta Arise TV a ranar Laraba, Gana ya ce, “Ni mai nazari ne, kuma ina nazarin ra’ayoyi, a jihohin Arewa Peter Obi a ƙarƙashin Jam’iyyar PDP zai doke duk wani ɗan takara, saboda mutanenmu suna da gaskiya.”

Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam

Peter Obi ya fice daga Jam’iyyar PDP a watan Mayun 2022 inda ya jagoranci Jam’iyyar LP a zaɓen 2023.

Da yake waiwayen tushen PDP, jigon na PDP ya tunatar da ’yan Najeriya irin ƙarfin da jam’iyyar ke da shi da kuma rawar da take takawa wajen maido da mulkin dimokraɗiyya.

Ya ce, “Dole ne in shaida cewa mutane da yawa sun manta cewa an kafa Jam’iyyar PDP ne a matsayin ƙungiya mai zaman kanta, a shekarar 1998 aka kafa mu, sannan muka shiga zaɓe a 1999, muna cikin kowace rumfar zaɓe, domin mu ne muka ci zaɓen farko.

“Mutane da yawa sun manta cewa PDP ce ta lashe mafi yawan ƙananan hukumomi, lokacin da aka zo batun zaɓen shugaban ƙasa, mun ci zaɓen shugaban ƙasa, mun ci na majalisar dattawa, muka ci majalisar tarayya, mu ne ke riƙe da madafun iko, shi ya sa muka yi matuƙar farin ciki da cewa mun maido da dimokuraɗiyya a Najeriya, muka sake kafa mulkin farar hula.

“Saboda shekaru da dama ana mulkin soja, amma mun samu nasarar kawo ƙarshen hakan ta hanyar dimokuraɗiyya, don haka PDP ta kasance jam’iyyar talakawa ce, shi ya sa idan muka ce mulki ga jama’a, muna nufin hakan ne saboda abin ya kasance, kuma ya kasance haka.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine