Iran: Himmati Yana Halattar Taro Dangane Da Matsalolin Da Suka Addabar Kasashe Masu Tasuwa
Published: 17th, February 2025 GMT
Ministan tattalin arziki na kasar Iran Abdunnaser Himmati yana halatan taro dangane da matsaloli da kuma dammakin da kasashen masu tasowa suka fama da su a birnin Riyad na kasar Saudiya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa Himmati yana halattan wannan taro na kwanaki biyu ne tare da gayyatar tokwaransa na kasar Saudiya da kuma shugaban asusun lamuni ta duniya wato IMF.
Labarin ya kara da cewa gwamnatin JMI dai tana kokarin ganin ta kyautata dangantaka ko ta ina da kasashen larabawa na yankin tekun da sauran makobta.
Taron ya hada da ministan kudi na kasar Saudiya, gwamnann babban bankin kasar, da kuma wadanda suke ruwa da tsaki a harkkin kasuwanci na kasar ta saudia, sun hadu da tokwarorinsa na Iran inda suka tattauna kan al-amuran tattalin arziki a tsakaninsu.
Himmati ya bukaci karin hadin kai da kasar saudiya don zuba jari a fannoni daban-daban a kasar Iran. Har’ila yau sun tattauna batun harkokin kudade a lokacin ayyukan hajji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
Tsohon ɗan wasan tsakiyar Barcelona, Carles Perez, yana kwance a asibiti a ƙasar Girka bayan da wani kare ya cije shi a al’aurarsa yayin da yake yawo da nasa karen a Thermi, a wata unguwa a Thessaloniki, ranar Talata.
Perez, mai shekaru 27, yana ƙoƙarin raba karensa da wani da suke fada lokacin da ya ji ciwo mai tsanani a wajen. An garzaya da shi zuwa wani asibiti mai zaman kansa a Panorama inda aka ɗinke masa raunin da ƙwayoyin da suka kai guda shida.
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa BarcelonaƘungiyar ƙwallon ƙafa ta Aris FC, wacce ta karɓi Perez aro daga Celta Vigo, ta tabbatar da cewa ya samu “cizon da ya haddasa kumburin naman wajen,” kuma hakan ya sa ba zai buga wasan UEFA Conference League da za su kara da Araz-Nakhchivan ranar Alhamis ba.
Kocin ƙungiyar, Marinos Ouzounidis, ya bayyana cewa an tsara Perez zai fara wasan kafin lamarin ya faru. “Carles zai kasance cikin ƴan wasa 11 na farko da zasu fara fafatawa” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp