Abu Ubaidah: Hamas Za Ta Saki Fursunoni 3 A Yau Asabar
Published: 15th, February 2025 GMT
Kakakin dakarun rundunar “Kassam” Abu Ubaidah ya sanar da cewa za su saki fursunoni 3 na “Isra’ilawa” a wannan rana ta Asabar.
A jiya Juma’a ne dai kakakin na dakarun rundunar “ Kassam” ya fitar da sanarwar cewa za saki fursunoni uku da suke rike da su da su ne: Shasha Alexander,Sagi Dikel Hen,Yaei Horun
A ranar Litinin din da ta gabata ne dai mai Magana da yawun dakarun na “Kassam” Abu Ubaidah ta sanar da dakatar da duk wani batu na cigaba das akin fursunonin sai illa masha Allahu.
Sai dai daga ranar Alhamis zuwa jiya Juma’a masu shiga tsakani da su ne kasashen Katar da Masar, sun yi kokarin gusar da matsalar da ta kunno kai daga gefen HKI da hakan ya bayar da damar sake komawa kan batun musayar fursunonin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun yi bayani kan sabon salon mayar da martani kan Isra’ila a harin ‘Alkawarin Gaskiya na 3″
Ma’aikatar hulda da jama’a ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran a cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin jiya Asabar ta sanar da cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage masu saukar ungulu a matsayin mayar da martani ga sabon farmakin da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan Iran.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar hulda da jama’a ta IRGC ta fitar ta bayyana cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon salon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” kan yankunan haramtaciyar kasar Isra’ila da muhimman cibiyoyinta ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuka don mayar da martani ga sabon harin wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan kasar Iran.