Ɗan majalisar Kebbi ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
Published: 12th, February 2025 GMT
Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Besse/Maiyama daga Jihar Kebbi, Salisu Garba Koko, ya sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Koko, ya sanar da wannan mataki ne cikin wata wasiƙa da ya aike kuma aka karanta a zauren majalisa.
N50,000 aka biya ni don safarar harsasai zuwa Abuja – Matashi Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — ZulumYa bayyana rikicin cikin gida a jam’iyyar PDP a matsayin dalilin da ya tilasta masa barin ta.
Wannan sauya sheƙa ya biyo bayan ficewar wani ɗan majalisar Kaduna, Amos Gwamna Magaji, wanda shi ma ya fice daga PDP sabida rikice-rikice.
Sai dai shugaban marasa rinjaye a majalisar, Kingsley Chinda, ya musanta zargin jam’iyyar na fama da rikice-rikice.
Ya jadadda cewar kowace jam’iyya tana da bambancin ra’ayi, amma hakan ba yana nufin samun rigingimu ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Sauya Sheƙa
এছাড়াও পড়ুন:
Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
Ɗaya daga cikin jigo da suka kafa Jam’iyyar PDP, Farfesa Jerry Gana ya yi iƙirarin cewa tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi zai kayar da duk wani ɗan takara a jihohin Arewacin Najeriya idan ya tsaya takara a PDP.
Da yake bayabni a tashar talabijin ta Arise TV a ranar Laraba, Gana ya ce, “Ni mai nazari ne, kuma ina nazarin ra’ayoyi, a jihohin Arewa Peter Obi a ƙarƙashin Jam’iyyar PDP zai doke duk wani ɗan takara, saboda mutanenmu suna da gaskiya.”
Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar KwastamPeter Obi ya fice daga Jam’iyyar PDP a watan Mayun 2022 inda ya jagoranci Jam’iyyar LP a zaɓen 2023.
Da yake waiwayen tushen PDP, jigon na PDP ya tunatar da ’yan Najeriya irin ƙarfin da jam’iyyar ke da shi da kuma rawar da take takawa wajen maido da mulkin dimokraɗiyya.
Ya ce, “Dole ne in shaida cewa mutane da yawa sun manta cewa an kafa Jam’iyyar PDP ne a matsayin ƙungiya mai zaman kanta, a shekarar 1998 aka kafa mu, sannan muka shiga zaɓe a 1999, muna cikin kowace rumfar zaɓe, domin mu ne muka ci zaɓen farko.
“Mutane da yawa sun manta cewa PDP ce ta lashe mafi yawan ƙananan hukumomi, lokacin da aka zo batun zaɓen shugaban ƙasa, mun ci zaɓen shugaban ƙasa, mun ci na majalisar dattawa, muka ci majalisar tarayya, mu ne ke riƙe da madafun iko, shi ya sa muka yi matuƙar farin ciki da cewa mun maido da dimokuraɗiyya a Najeriya, muka sake kafa mulkin farar hula.
“Saboda shekaru da dama ana mulkin soja, amma mun samu nasarar kawo ƙarshen hakan ta hanyar dimokuraɗiyya, don haka PDP ta kasance jam’iyyar talakawa ce, shi ya sa idan muka ce mulki ga jama’a, muna nufin hakan ne saboda abin ya kasance, kuma ya kasance haka.”