Aminiya:
2025-05-28@04:46:09 GMT

An kama ’yan ina-da-kisa 47 a Kwalejin Tarayya a Kebbi

Published: 11th, February 2025 GMT

’Yan sanda sun kama gungun wasu makiyaya 47 ɗauke da makamai kan zargin kutse da yunƙurin aikata kisa a Kwalejin Kimiyya da Ƙere-kere ta Tarayya ta Umaru Waziri da ke Shinkafi a Jihar Kebbi.

Kakakin ’yan sandan Jihar Kebbi, CSP Nafi’u Abubakar ya ce makiyayan sun haɗa baki ne da wani mutum wajen rusa katangar makarantar suka kutsa cikinta da garken shanu sama da 300.

Ya ce da shigarsu ke da wuya. sai suka zarce zuwa ɓangaren gidajen ma’aikata suka lalata musu haki.

Ya ƙara da cewa makiyayan sun kuma sari wani jami’in tsaron makarantar da adda a ƙafarsa ta dama a hannunsa na dama.

Dalibai 179 sun kammala Dirigi da Daraja ta Ɗaya a Jami’ar Bayero Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga

“A sakamakon haka ya samu karaya a ƙafar damsa kuma yanzu ana jinyar sa a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Birnin Kebbi,” in ji CSP Nafi’u Abubakar.

Ya ce Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kebbi, Bello M Sani, ya jagoranci tawagar masu bincike zuwa wurin domin tantance abin da ya faru.

Sanarwar ta ce, “A yayin da ake ci gaba da bincike, mutum 47 daga cikinsu sun riga sun shiga hannu kuma nan gaba za a gurfanar da su a kotu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano

Hukumar Kwastam reshen Kano da Jigawa, ta kama nau’in ƙwayar Tiramol katan 491,000, tare da miƙa su ga Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC).

An ƙiyasta kuɗin magungunan da aka kama sama da Naira miliyan 150, kuma an gano su a cikin wata mota ƙirar Lexus SUV, a hanyar Gumel zuwa Maigatari da ke Jihar Jigawa.

FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

Kwanturolan hukumar a yankin, Dalhatu Abubakar, ya ce an yi wannan nasara ne bisa sahihan bayanan sirri, kuma yana daga cikin ƙoƙarin da suke yi tun bayan shigarsa ofis a watan Fabrairun 2025.

Abubakar, ya ce an shigo da ƙwayoyin ne cikin dare, kuma sun saɓa da dokokin da aka sarrafa su.

“Wannan ƙwaya tana lalata rayuka. Ka tambayi kanka shin wata ’yar uwarka, ɗanka, ko maƙwabcinka ba sa amfani da ita?” in ji shi.

Ya ƙara da cewa amfani da Tiramol yana haifar da ƙaruwar laifuka, taɓin hankali, da rashin tsaro, musamman a Arewacin Najeriya.

Bisa ƙididdigar da Majalisar Ɗinkin Duniya da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) suka fitar, ana ƙiyasta cewa kimanin mutane miliyan uku ke amfani da miyagun ƙwayoyi a yankin Arewa maso Yamma.

A Jihar Kano kuwa, sama da mutum 670,000 ke amfani da ƙwayar Tiramol ba tare da izinin likita ba.

Ya kuma ce daga cikin masu amfani da ƙwayoyi a Najeriya huɗu mata ne, wanda hakan abin damuwa ne ganin rawar da mata ke takawa a cikin gida da al’umma.

Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa daga wajen malamai, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula, da hukumomin gwamnati don yaƙi da matsalar amfani da miyagun ƙwayoyi.

Taron ya ƙare ne da miƙa ƙwayoyin da aka kama zuwa hannun Hukumar NAFDAC domin ɗaukar matakin doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno
  • ’Yan sanda sun kama wanda ake zargi da kisan matar aure a Kano
  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a
  • Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
  • Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano
  • Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wanda Ya Kona Masallata A Kano
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu
  • Ya Kubuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja